Labaran garkuwa da mutane
Wani dan sanda mai gaskiya yaki karbar Naira miliyan 1 da wani ya bashi matsayin cin hanci don sakin wani Yusuf Ibrahim da aka kama kan garkuwa da mutane a Kano
Labarin da muke samu ya ce, sojoji sun ceto wasu mutanen da 'yan bindiga suka sace suka tafi dasu. An hallaka 'yan bindiga uku nan take yayin kwanton bauna.
A wani labari mai dauke da jimami, wasu 'yan bindiga sun sace amare guda biyu a jihar Neja, sun kuma yi awon gaba da wasu mutane 47 yayin da suka kai hari.
Wasu tsagerun yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun fille kan Chris Ohizu, shugaban karamar hukumar Ideato ta arewa a jihar Imo bayan sun karbi miliyan 6.
Wasu miyagun ‘yan bindiga sun kai farmaki wani yankin karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi.‘Yan bindiga sun halaka rayuka biyar sannan sun sace mutum 1.
An samu tsaiko a wata jihar Kudu yayin da wasu 'yan bindiga suka farmaki mambobin jam'iyyar APC a lokacin da suke tsaka da gudanar da taron jam'iyyar a jihar.
Wasu miyagun ‘yan bindiga sun kai farmaki gidan basarake kuma tsohon alkali a cikin Jalingo. Sun yi garkuwa da matansa biyu tare da tasa keyar ‘ya’yansa shida.
Yanzu muke samun mummunan labarin yadda wasu tsagerun 'yan bindiga suka sace daliban makarantar firamaren gwamnati a wata jihar Arewa, jihar Nasarawa a Arewa.
hukumar NSCDC a jihar kaduna ta bayyana bukatar dangi su fito domin maye gurbin jami'anta 7 da aka kashe a wata arangama da tsagerun 'yan bindiga a jiha Kaduna.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari