Rikcin makiyaya a Najeriya
'Yan bindiga sun kashe jigon APC da wasu mutum uku a Benue a wani harin kwantan bauna da suka kai garuruwa biyu. An ce wannan ne hari na biyu a cikin makonni biyu.
Jakadan Amurka a Najeriya, Richard Mills ya gana da kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah domin jin matsalolin makiyaya a yankunan Najeriya da samar da mafita.
Kungiyar makiyaya ta sanar da cewa an kai hari kan shanu da wani makiyayi a karamar hukumar Riyom ta jihar Filato inda aka kashe shanu 37 da bindiga.
Ana fargabar cewa Fulani makiyaya sun kai hari a garin Gbagir, jihar Benue da safiyar Juma’a, sun kashe Kiristoci 10, sun jikkata 25, yayin da gwamnati ta yi martani
Gwamnatin Filato ta fara bincike kan saka guba wa shanun wani makiyayi a karamar hukumar Bassa. An kafa kwatin bincike domin tabbatar da gaskiyar lamarin.
Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya bayyana cewa ba rikicin manoma da makiyaya ne ke jawo asarar rayuka a jiharsa ba, ya ce akwai masu ɗaukar nauyi a gefe.
Hare-haren da aka kai kan garuruwa biyar a Bokkos sun yi sanadiyyar mutuwar mutum goma. BCDC ta yi kira ga jama’a su kare kansu daga barazanar ‘yan ta’adda.
Rundunar 'yan sanda a jihar Zamfara ta kama mutum 15 bayan Fulani makiyaya sun gwabza fada mai muni da Hausawa. An samu gawar wani matashi cikin jini.
Akalla mutum 1 aka tabbatar ya mutu da faɗa ya ɓarke tsakanin mutanen gari da makiyaya, waɗanda suka suka yi ƙoƙarin shayar da shanunsu ruwan da mutane ke sha.
Rikcin makiyaya a Najeriya
Samu kari