
Ahmad Lawan







Ahmad Lawan, shugaban majalisar dattawa ya sanar da dage zaman majalisar daga yau Laraba har zuwa ranar 25 ga watan Afrilu don ba da hutun Easter da Sallah.

Osita Izunaso ya ce ya cancanta ya zama shugaban majalisar dattawa da za a rantsar a Yuni. Sanatan na Imo ya hango kan shi a kujerar Shugaban Majalisa a 2023.

Muhammadu Buhari ya kawo dokar da za ta sa Gwamnatin tarayya ta kebe wasu gandun jeji. Da Hon. Alhassan Doguwa ya kawo maganar a zauren majalisa ta samu karbuwa

Rotimi Akeredolu da Yahaya Bello za su goyi bayan takarar Ahmed Idris Wase a Majalisar Wakilai, sun rabu da Abbas Tajuddeen wanda shi ne 'Dan takarar El-Rufai

Barau Ibrahim Jibrin ya shiga sahun wadanda za su nemi shugabancin Majalisar Dattawa. Da yiwuwar Sanatan Arewacin Kano ya gwabza da Orji Uzor Kalu a takarar.

‘Yan Majalisa da yawa sun rasa Kujerunsu a 2023. Shugaban majalisar wakilan tarayyan Femi Gbajabiamila ya zargi masu zabe da amfani da addini da kabilanci.

'Yan Majalisa 7 Daga Jihohin Arewa su na neman kujerar shugabancin majalisar wakilan tarayya ganin cewa zai yi wahala Femi Gbajabiamila ya zarce a karo na biyu.

Mun kawo cikakken jerin ‘Yan siyasan da INEC ta ba takardar shaidar lashe zaben Majalisa. Mata 2 rak su ka shiga jerin ‘Yan siyasa 109 da za su zama Sanatoci.

Alhassan Ado Doguwa yana sha’awar zama Shugaban majalisa, sannan Sani Musa, Barau Jibrin, Orji Uzor Kalu, Godswill Akpabio su na harin kujerar Ahmad Lawan.
Ahmad Lawan
Samu kari