Cikakken Bincike
Hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta'annati (EFCC) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello, a matsayin wanda take nema ruwa a jallo.
Hukumar EFCC ta yi barazanar yin amfani da jami'an sojoji domin cafke tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, wanda ya ki yarda jami'an hukumar su kama shi.
Binciken kwa-kwaf ya tabbatar babu gaskiya kan jita-jitar da ake yadawa cewa Betty Akeredolu, matar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu ta auri kaninsa.
Idan tsohon ministan wuta ya yi nasara, za a biya shi diyyar N1bn a kan binciken aikin Mambilla. Lauyoyi sun garzaya kotu a Abuja, sun yi karar AGF da EFCC.
Za a toshe asusu miliyan 70 saboda rashin BVN da NIN a Najeriya. CBN ya bda umarin a rufe duk asusun da aka samu bai da lambobin banki na BVN ko NIN.
A shari’arsa da EFCC, Babbar Kotun Tarayya ta bayar da umarnin kwace Naira biliyan 1.58 daga tsohon Manajan Darakta na Hukumar NIRSAL, Aliyu Abatti Abdulhameed.
Akwai mutane akalla 3 da ake zargi sun taimaka aka sace kusan N3tr daga CBN. Jami’an tsaro za su fara farautar Adamu Abubakar, Imam Abubakar da Odoh Ochene a duniya.
Za a samu labarin yadda Hukumar NDLEA mai yaki da safara da harkar miyagun kwayoyi ta damke wani Ahmed Mohammed da wasu mutane dauke da tulin kwayoyi.
EFCC tana binciken wasu manya, akwai yiwuwar nan gaba kadan a koma kotu. Zargin karkatar da kudi da rashin gaskiya da ke kan wadannan manya ya kai N853.8bn.
Cikakken Bincike
Samu kari