An Bazo Wa Minista Wuta, Hadimin Atiku Ya Bukaci Shugaba Tinubu Ya Tsige Shi Nan Take

An Bazo Wa Minista Wuta, Hadimin Atiku Ya Bukaci Shugaba Tinubu Ya Tsige Shi Nan Take

  • Hadimin tsohon mataimakin shugaban kasa, Paul Ibe ya ce bai kamata Uche Nnaji ya ci gaba da zama a kujerar Ministan Kimiyya da Fasaha ba
  • Mai magana da yawun Atiku ya bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sauke Ministan kuma ya mika shi domin a gurfanar da shi a kotu
  • Wannan dai na zuwa ne bayan bincike ya bankado cewa takardun Uche Nnaji na kammala digiri da bautar kasa watau NYSC duk na bogi ne

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Zargin amfani da takardun bogi da ake yi wa Ministan Kimiyya da Fasaha, Cif Uche Nnaji na kara tayar da kura a Najeriya.

Paul Ibe, Hadimin tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya ce kamata ya yi Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tsige ministan daga mukaminsa nan take.

Kara karanta wannan

Digirin bogi: An nemi Ministan Tinubu ya yi murabus, ya mika kansa ga hukuma

Shugaba Tinubu da Uche Nnaji.
Hoton Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji. Hoto: @aonanuga1956, @chiefuchennaji
Source: Twitter

Paul Ibe, mai magana da yawun Atiku ya bayyana haka ne a wani gajeren sako da ya wallafa shafinsa na Facebook yau Litinin, 6 ga watan Oktoba, 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An bazo wa Ministan Tinubu wuta

Wannan dai na zuwa ne bayan bincike ya bankado cewa ministan ya gabatar da satifiket din kammala digiri na bigi ga Shugaba Bola Tinubu da Majalisar Dattawa yayin tantancewa.

Binciken, wanda jaridar Premium Times ta wallafa ranar Asabar da ta gabata ya nuna cewa takardar digiri da takardar NYSC da Ministan ke amfani da su duk na bogi ne.

An fara zargin Uche Nnaji da amfani da takardun bogi tun a watan Yuli 2023, lokacin da Shugaba Tinubu ya sa sunan Nnaji a cikin jerin ministoci 28 na farko da aka tura majalisar dattawa.

Bayan bayyanar wannan bincike a karshen makon jiya, yan adawa a Najeriya suka fara kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sauke Nnaji daga kujerar minista.

Kara karanta wannan

ADC ta tanka zargin da ake yi wa ministan Tinubu na yin amfani da takardun bogi

Hadimin Atiku ya nemi a kori Uche Nnaji

Da yake martani kan lamarin, hadimim Atiku, Paul Ibe ya ce bai kamata Shugaba Tinubu ya bar ministan a kan kujerarsa ba.

A cewarsa, ya dace Shugaban Kasa ya tsige ministan daga mukaminsa, sannan ya mika shi ga hukumomi domin a gurfanar da shi a gaban kuliya.

"Tun da Jami’ar Najeriya ta Nsukka (UNN) ta tabbatar da cewa Minista, Uche Nnaji na amfani da takardar shaidar digiri ta bogi, wacce ita ya gabatar lokacin da aka nada shi minista, bai kamata ya ci gaba da zama ba.
"Mu na tsammanin cewa Shugaba Bola Tinubu zai tsige shi daga mukaminsa tare da mika shi ga hukuma domin gurfanar da shi a gaban kotu."
Paul Ibe tare da Atiku.
Hoton Paul Ibe tare da maigidansa, Alhaji Atiku Abubakar. Hoto: Paul Ibe
Source: Twitter

Ministan Tinubu zai fito ya kare kansa

A wani rahoton, kun ji cewa Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji ya yanke shawarar fitowa ya kare kansa kan zargin da ake masa na amfani da takardun bogi.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Ministan Tinubu zai fito bainar jama'a kan zargin amfani da digirin bogi

Bayanai sun nuna cewa Nnaji zai yi magana kan lamarin a taron manema labarai da ya kira a ranar Litinin, 6 ga watan Oktoba, 2025 a Abuja.

Hakan ma zuwa ne bayan an yiwa Ministan ca kan batun takardun bogi, lamarin da aka fara zarginsa da shi tun nada shi a mataayin Minista.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262