Ta Fara Tsami tsakanin Gwamna da Ministan Tsaro, APC Ta Fusata kan Lamarin

Ta Fara Tsami tsakanin Gwamna da Ministan Tsaro, APC Ta Fusata kan Lamarin

  • Jam’iyyar APC ta gargaɗi mambobinta su guji tayar da fitintinu, musamman masu goyon bayan tsohon gwamna, Mohammed Badaru Abubakar
  • An gargadi yaran da ake kira “Badaru Boys” da haddasa rikice-rikice a wuraren taruka da zaben cike gurbi
  • Har ila yau, ana zargin yaran suna kuma ɓata sunan Gwamna Umar Namadi wanda hakan rashin ladabi ne

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Dutse, Jigawa - Jam’iyyar APC a Jigawa ta yi gargaɗi ga wasu mambobinta kan kokarin jawo hatsaniya a jihar.

Jam'iyyar ta bukaci mambobinta su guji rashin ɗa’a da halaye marasa kyau da za su iya kawo rabuwar kai.

Jam'iyyar APC za ta shata layi kan magoyan bayan Badaru a Jigawa
Gwamna Umar Namadi da ministan tsaro, Mohammed Abubakar Badaru. Hoto: Umar Namadi, Mohammed Badaru.
Source: Facebook

Hakan na cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar, Muhammad Dikuma Umar ya sa hannu wanda Aminiya ta samu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Zargin matsala tsakanin Badaru da Gwamna Namadi

Hakan ya biyo bayan zargin akwai matsala tsakanin Gwamna Umar Namadi da tsohon gwamnan jihar, Mohammed Badaru Abubakar.

Kara karanta wannan

'Yan sandan jihohi: Gwamnonin Arewa sun hade, sun mara wa kudirin Tinubu baya

A yanzu haka, Badaru shi ne babban ministan tsaro a Najeriya bayan Bola Tinubu ya hau mulki a watan Mayun 2023.

Kamar yadda yake faruwa a wasu jihohi, an ce akwai alamun baraka ta barke a jam'iyyar APC da ke jihar Jigawa.

Wasu rahotanni sun ce alaka ta fara tsami tsakanin tsohon gwamnan jihar, Badaru Abubakar da Gwamna Umar Namadi.

Sai dai gwamnan jihar ya yi magana kan lamarin inda ya ce babu wata baraka musamman a jam'iyyar APC amma ya tabbatar wasu na kitsa ta.

APC ta fusata kan halayen yaran Badaru

Jam'iyyar ta ce wasu magoya bayan tsohon gwamna Mohammed Badaru Abubakar da ake kira “Badaru Boys” suna tayar da hankali.

An zargi “Badaru Boys” da rikice-rikice a Majiya da ke Gumel da zaben Babura/Garki, tare da cin fuska ga gwamnati a taron Kafin Hausa.

APC ta fusata kan halayen magoya bayan Badaru a Jigawa
Gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi Dan Modi. Hoto: Umar Namadi.
Source: Facebook

APC ta kare Gwamna Namadi a Jigawa

Jam’iyyar ta ce, duk da rashin ladabi, Gwamna Namadi ya yi haƙuri, amma ta koka da yadda tsohon gwamna bai tsawatar da magoya bayansa ba.

Kara karanta wannan

'Namadi ya zamo gwarzo,' Jigon APC, Mahmood ya jero alherin gwamnan Jigawa

“Fitinar ‘Badaru Boys’ ta yi yawa, Wannan ɗabi’a… ta sabawa sashe na 21 na kundin tsarin mulkin APC."

- Cewar sanarwar

APC ta yi barazanar amfani da kundin mulki don ladabtarwa, ta kuma kira jami’an tsaro su dauki mataki don hana ɓarkewar rikicin siyasa.

Wasu na ganin wannan baraka na iya jawo matsala ga jam'iyyar a zaben 2027 da ake tunkara wanda yake da matukar tasiri.

Sai dai gaggawar daukar mataki da jan kunne zai iya kawo karshen matsalar da ke tunkarar APC a jihar.

Gwamna Namadi ya kwarara yabo ga Tinubu

Mun ba ku labarin cewa gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, ya ƙwarara yabo ga shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

Umar Namadi ya bayyana cewa shugaban ƙasar ya nuna jarumtaka wajen ɗaukar matakan da waɗanda suka gabace shi suka kasa ɗauka.

Ya nuna cewa matakan da Tinubu ya ɗauka sun taimaka wajen farfaɗo da tattalin arziƙin Najeriya wanda ya kama hanyar durƙushewa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.