An Zo Wajen: Wike Ya Fadi Lokacin da Gwamna Fubara Zai Dawo kan Mulki a Rivers
- Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya kada kuri'arsa a zaben kananan hukumomin jihar Rivers
- Nyesom Wike ya yaba kan yadda zaben yake gudana cikin kwanciyar hankali da lumana a sassa daban-daban na jihar
- Ministan ya kuma nuna cewa akwai yiwuwar Gwamna Siminalayi Fubara da 'yan majalisar dokokin jihar su koma kan kujerunsu a watan Satumba
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Rivers - Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya yi magana kan lokacin dawowar Gwamna Siminalayi Fubara kan mukaminsa.
Nyesom Wike ya bayyana cewa Gwamna Siminalayi Fubara tare da ’yan majalisar dokokin jihar za su koma bakin aikinsu ranar 18 ga watan Satumban 2025, lokacin da dokar ta-baci a Rivers za ta kare.

Source: Facebook
Jaridar Daily Trust ta ce Wike ya faɗi haka ne a ranar Asabar, jim kaɗan bayan ya kada kuri’arsa a zaɓen kananan hukumomi da ake gudanarwa a jihar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Wike ya kada kuri'a a zaben Rivers
Ministan ya kada kuri’a a rumfar zaɓe ta bakwai, mazaba ta tara a kauyen Rumuepirikom, karamar hukumar Obio-Akpor.
Bayan ya kada kuri’a, Wike ya yi watsi da damuwar da ake nunawa kan rashin fitowar jama’a da kuma rashin amfani da na’urar tantance masu kada ƙuri’a (BVAS) a zaɓen.
"Ina matukar farin ciki. Wannan yana nuna cewa jama’a sun amince da zaɓen. Ba ku ji labarin tashin hankali ba, ba ku ji labarin ɗaukar akwatin kada kuri’a ba."
"Kamar yadda ku ke gani, kayan zaɓe sun iso, mutane suna nan suna kada ƙuri’a. A ganina wannan zaɓe yana gudana cikin lumana.”
- Nyesom Wike
Dangane da rashin amfani da BVAS, Wike ya ce hakan bai rage ingancin zaɓen ba, rahoton jaridar TheCable ya tabbatar da wannan.
"Tabbas, mun damu da karancin fitowar jama’a, amma mutane suna ci gaba da fitowa. Kafin zaɓe ya ƙare, za ku ga adadin masu kada ƙuri’a ya ƙaru. Don haka muna farin ciki ƙwarai da yadda wannan zaɓe ya gudana cikin nasara da lumana."
- Nyesom Wike
Yaushe gwamna Fubara zai dawo kan mulki?
Ministan ya danganta nasarar gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi da yiwuwar janye dokar ta-baci da Shugaba Bola Tinubu ya ayyana a jihar a farkon shekarar nan.

Source: Twitter
Ya ce idan ba a gudanar da zaɓen kananan hukumomi karkashin dokar ta-baci ba, hakan zai sanya ba za a samu shugabanci ba a matakin kasa bayan janye dokar.
"Ma’anar wannan zaɓe shi ne ku sani cewa daga ranar 18 ga Satumba, dokar ta-baci za ta kare, gwamna da ’yan majalisar dokokin jiha za su koma bakin aikinsu."
"Kuma ku tuna cewa Kotun Koli ta soke zaɓen da ya gabata. Idan aka kasa gudanar da wannan zaɓe, hakan zai nuna babu mulki a matakin kananan hukumomi.”
- Nyesom Wike
Hadimin Wike ya caccaki jam'iyyar PDP
A wani labarin kuma, kun ji cewa mai magana da yawun bakin ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya caccaki jam'iyyar PDP.
Lere Olayinka ya soki PDP ne kan matakin da ta dauka na kai tikitin shugaban kasa zuwa yankin Kudu a zaben 2027.
Ya bayyana cewa jam'iyyar ta makara domin tun a zaben 2027 ya kamata ta yi hakan, lokacin da Wike ya ba ta shawara.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


