2027: Gwamnonin PDP 8 Sun Tsayar da Abin da Suke Yi, Sun Nufi Jihar Zamfara

2027: Gwamnonin PDP 8 Sun Tsayar da Abin da Suke Yi, Sun Nufi Jihar Zamfara

  • Gwamnonin jam'iyyar PDP sun shirya gudanar da taro a jihar Zamfara ranar Asabar, 23 ga watan Agusta, 2025 a jihar Zamfara
  • Gwamna Dauda Lawal zai karbi bakuncin gwamnonin a yau Juma'a, inda za su halarci liyafar da aka shirya kafin taron da za su yi washe gari
  • Ana ran gwamnonin jihohin Bauchi, Taraba, Filato, Bayelsa, Enugu, Adamawa, Osun da Oyo za su yi taro a garin Gusau a ranar Asabar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Zamfara - Gwamna Dauda Lawal zai ya karɓi bakuncin gwamnonin da aka zaɓa a karkashin jam’iyyar PDP domin gudanar da wani muhimmin taro a jihar Zamfara.

Kungiyar gwamnonin PDP ta shirya taron ne a ranar Asabar, 23 ga watan Agusta, 2025 a Jihar Zamfara, daya daga cikin jihohin da ke hannun jam'iyyar hamayya a yau.

Kara karanta wannan

Lokaci ya yi: Sarki mai martaba a Najeriya ya rasu yana mai shekaru 89

Gwamnonin PDP.
Hotom gwamnonin PDP a wani taro da suka yi a Ibadan, jihar Oyo Hoto: @seyiamakinde
Source: Twitter

Gwamnoni PDP 8 za su dura jihar Zamfara

Rahotan Leadership ya bayyana cewa, ana sa ran gwamnonin PDP takwas za su isa Gusau, babban birnin Zamfara da yammacin yau Juma’a, 22 ga watan Agusta, 2025.

Gwamnonin za su hadu da Gwamna Dauda Lawal domin halartar liyafa ta musamman kafin taron da aka tsara zai gudana da safiyar ranar Asabar.

Hakan dai na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a Gusau.

Sanarwar ta bayyana cewa, gwamnonin PDP za su tattauna muhimman dabarun siyasa yayin da suke kokarin shawo kan kalubalen rikicin da ake ciki a jam'iyyar a yanzu.

Abubuwan da gwamnonin PDP za su tattauna

“Gwamna Dauda Lawal na mika gaisuwa da maraba ga takwarorinsa, gwamnonin jam’iyyar PDP da za su hallara a Zamfara domin taron kungiyar gwamnonin PDP."
"Za a gudanar da liyafa ta musamman da Gwamna Dauda Lawal ya shirya wa gwamnonin a daren yau, kafin taron sirri da aka tsara yi idan Allah ya kaimu gobe.

Kara karanta wannan

An dauki gwamna 1 a Najeriya, an ba shi lambar yabo ta 'Zabin Jama'a' a kasar Faransa

“Taron zai ba jagororin jam’iyyar damar tattauna batutuwan siyasa masu muhimmanci, tsara matakan hada kan PDP, da kuma yadda za su kawo ci gaba a jihohinsu.
"Za su tattauna kan batutuwan da suka shafi shirin babban taron PDP na kasa da aka shirya a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, 2025.”

- In ji Sulaiman Bala Idris.

Gwamna Dauda Lawal.
Hoton Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara a fadar gwamnatinsa Hoto: Dauda Lawal
Source: Twitter

Gwamnonin da ake sa ran za su isa Zamfara

Gwamnoni takwas da ake sa ran Gwamna Dauda zai karbi bakuncinsu sun hada da Bala Mohammed (Bauchi), Agbu Kefas (Taraba), Caleb Mutfwang (Filato) da Seyi Makinde (Oyo).

Sauran su ne, Ademola Adeleke (Osun), Douye Diri (Bayelsa), Peter Mbah (Enugu), da Ahmadu Fintiri (Adamawa), kamar yadda Vanguard ta rahoto.

Gwamnonin PDP 2 sun amince da tazarcen Tinubu

A wani labarin, kum ji cewa gwamnonin jam'iyyar PDP guda biyu sun fito karara sun bayyana goyon bayansu ga tazarcen Bola Tinubu a 2027.

Gwamnonin sun tabbatar da cewa za su marawa Shugaba Tinubu domin ya kammala wa'adin mulki na biyu karkashin APC duk da ba jam'iyyarsu ɗaya ba.

Wannan dai na kara nuna yadda jam'iyyar PDP ke fama da rikicin cikin gida, wanda ya hana ta zama lafiya tun bayan zaben 2023.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262