SDP Ta Fice daga Haɗakarsu Atiku, Za Ta Fito da Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a 2027

SDP Ta Fice daga Haɗakarsu Atiku, Za Ta Fito da Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a 2027

  • Jam’iyyar SDP ta karbe rikon NWC daga hannun Shehu Musa Gabam, sakamakon rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar
  • Kwamitin NEC ya nada sababbin shugabannin rikon kwarya da za su tafiyar da SDP har zuwa lokacin da za a yi zaben jam'iyyar
  • NEC ya kuma sanar da ficewar SDP daga hadakar siyasa da Atiku Abubakar ke jagoranta, inda jam’iyyar ta ce za ta tsaya takara a 2027

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja – Rikicin cikin gida da ke addabar SDP ya dauki sabon salo ranar Juma’a, yayin wani zaman kwamitin majalisar zartaswar jam’iyyar na kasa (NEC).

A yayin zaman, NEC din ya rushe shugabancin kwamitin da Shehu Gabam ke jagoranta, wanda aka dakatar a baya, saboda rikicin cikin jam’iyyar.

Jam'iyyar SDP ta rusa shugabanninta da ke karkashin Shehu Musa Gabam, ta zabi wasu
Wasu daga cikin jagororin SDP na magana da mema labarai a ofishin jam'iyyar na Abuja. Hoto: @Pres_Adebayo
Source: UGC

SDP ta rushe shugabannin jam'iyya na kasa

Kara karanta wannan

Jim kadan da nadin shugabanta na kasa, APC ta yi sababbin sauye sauye a NWC

Wannan mataki ya fito ne a taron gaggawa da NEC din SDP ya gudanar a Abuja, wanda sakataren kudi na kasa na jam’iyyar, Ibrahim Biu, ya jagoranta, inji rahoton Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ibrahim Biu ya bayyana cewa:

“Daga wannan lokaci, an rusa kwamitin gudanarwa na kasa. Mun naɗa wadannan mutane da za su rike shugabancin jam’iyyarmu mai girma, kuma su ci gaba da tafiyar da ita gaba.”

Sababbin shugabannin rikon kwarya da aka nada sun hada da:

  1. Adamu Modibo - Shugaban rikon kwarya na kasa
  2. Abubakar Dogara - Mataimakin shugaba
  3. Ekpeyong Ambo - Sakataren jam'iyya na kasa
  4. Joseph Abu - Sakataren shirye-shirye na kasa
  5. Chief Solsuema Osaro - Mai ba da shawara kan harkokin doka
  6. Judith Shuaibu - Sakatariyar yada labarai ta kasa
  7. Ibrahim Biu - Sakataren kudi na kasa
  8. Eluwa Ifeanyi - Mai magana da yawun matasa na kasa

Rikicin da ya dabaibaye jam'iyyar SDP

Biu ya shaida wa manema labarai cewa:

"Tabbas, abin takaici ne NEC ta dauki wannan mataki mai tsauri bayan shawarwari da dama da aka yi domin warware rikicin da suka ci tura.

Kara karanta wannan

Ana fargabar El Rufai, Peter Obi na iya ficewa daga hadaka saboda burin Atiku

“A ‘yan watannin baya, jam’iyyar mu ta fada cikin rikicin shugabanci. Kamar yadda kuka sani, jam’iyyar ta dare gida biyu.
“Wannan ya jawo tashin hankali a jam'iyyar, har ma bangarorin biyu suka yi arangama a hedikwatar SDP, wanda hakan ya sa jami’an tsaro suka shiga tsakani.”

"SDP ba ta cikin hadaka" - Dogara

A wani bangare na taron, kwamitin NEC ya bayyana ficewar SDP daga hadakar su tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da ke karkashin jam’iyyar ADC.

Jam'iyyar SDP ta ce ta fita daga hadakarsu Atiku Abubakar kuma za ta shiga zaben 2027
Lokacin da Nenadi Usman da sauran jagororin SDP suka yiwa Nasir El-Rufai maraba da shiga jam'iyyar. Hoto: Senator Nenadi Usman
Source: Facebook

TVC News ya rahoto mataimakin sabon shugaban jam’iyyar, Abubakar Dogara, ya fayyace matsayin SDP da cewa:

“Kwanan nan an yi yunkurin hadin gwiwa tsakanin manyan ‘yan siyasa da jam’iyyu domin samar da hadaka, wanda SDP ta shiga tun farko.
"Sai dai daga baya, wakilin SDP a taron ya bayyana wa 'yan hadakar cewa SDP na cikin shirye-shiryen tunkarar zabukan cike gurbi a jihohi 12, kuma ba za ta so ta rasa martabarta ba.
“Don haka, SDP ba ta cikin wannan hadaka. Za mu fito da dan takarar shugaban kasa da mataimaki daga SDP a zaben 2027 mai zuwa.”

Kara karanta wannan

Jam'iyyar PDP ta haƙura da Kano, ta sauya wuri da ranar gudanar da babban taron ƙasa

Kallo taron jam'iyyar a kasa:

'Ba mu tura El-Rufai hadaka ba' - SDP

A wani labarin, mun ruwaito cewa, 'dan takarar shugaban kasa na SDP a 2023, Adewole Adebayo ya ce jam'iyyarsu ba ta da wakili a haɗakar ƴan adawa.

Adebayo ya yi ikirarin cewa SDP ba ta tura Nasir El-Rufai ya wakilce ta a hadakar da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar yake jagoranta.

Tun bayan samun saɓani da fadar shugaban kasa da APC, tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya tattara ya koma jam'iyyar SDP.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com