Tuna Baya: Abin da Ya Rusa Haɗakar Obasanjo a ADC domin Yakar Buhari a 2019

Tuna Baya: Abin da Ya Rusa Haɗakar Obasanjo a ADC domin Yakar Buhari a 2019

  • A shekarar 2018, tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya jagoranci kafa hadaka da nufin kawo sauyi a kasa
  • Hadakar ta rungumi jam’iyyar ADC a matsayin dandalin siyasa wanda ke kokarin kwace mulki a hannun Muhammadu Buhari
  • Bayan watanni uku, CNM ta rabu da ADC saboda rashin fahimta kan hadin gwiwa da CUPP wanda ya jawo rikici da rabuwar kai

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - Yayin da yan adawa suka rungumi ADC domin kifar da gwamnatin Bola Tinubu, wannan ba shi ne karon farko ba.

A watan Mayun 2018, an kafa kawancen siyasa da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya kirkiro ta rungumi jam'iyyar ADC.

Hadakar Obasanjo a ADC ta rushe a wata 3
Obasanjo ya shirya haɗaka domin kwace mulkin Buhari a 2019. Hoto: Olusegun Obasanjo, Muhammadu Buhari.
Source: Twitter

2019: Hadakar da Obasanjo ya shirya domin doke Buhari

Jaridar TheCable ta ce an yi hakan ne domin kalubalantar shugaba Muhammadu Buhari a zaben 2019.

Kara karanta wannan

Plateau: Yayin da ake watsewa Tinubu, hadimin gwamna ya ajiye aiki, ya dawo APC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kungiyar da Obasanjo ya jagoranta 'Coalition of Nigeria Movement (CNM)' ta bayyana ADC a matsayin jam’iyyar adawa ga Buhari.

Daga cikin mahalarta taron sun hada da Obasanjo, Olagunsoye Oyinlola, wanda shi ne mai daukar nauyin kungiyar kuma tsohon gwamnan jihar Osun da wasu ‘yan siyasa.

Obasanjo ya gabatar da CNM a matsayin wata kafa maras bangaranci da za ta “kubutar” da Najeriya daga wahalhalun da gwamnatin Buhari ta jawo.

Ya ce kungiyar ta rungumi ADC ne don samar da sauyin da ake bukata a siyasar Najeriya da shugabanci, cewar Premium Times.

Tsohon shugaban ya bayyana cewa jam'iyyar ADC ba ta da alaka da “halin baya na PDP” da kuma “mummunan tafiyar APC.”

"Zan fara da taya murna da jinjina ga farfadowar jam’iyyar African Democratic Congress, ADC, a matsayin jam’iyyar siyasa.
"Tun bayan kafuwar CNM, jam’iyyu 68 sun tuntubi kungiyar kan yadda za a hada kai da aiki tare.

Kara karanta wannan

Ministan Buhari, Malami ya fice daga APC, ya zaɓi sabuwar jam'iyyar haɗaka

"Shugabannin kungiyar, bayan tantancewa da shawarwari masu zurfi da la’akari da manufofin kungiyar, sun amince da rungumar ADC don kawo sauyi."

- Cewar Obasanjo

Hadakar kifar da Buhari ta rushe kafin wata 4
Obasanjo ya shirya hadakar kwace mulkin Buhari kafin ta watse a wata 3. Hoto: Muhammadu Buhari.
Source: Twitter

Tsawon lokaci da hadakar Obasanjo ta dauka

Haka kuma, Oyinlola ya ce shigar su cikin ADC ya nuna godiya ga cigaban siyasar jam’iyyar da zaman lafiyar ta a harkokin siyasar Najeriya.

Tsohon gwamnan ya ce 'yan Najeriya su sa ran karin abubuwa daga kungiyar, yana kiran hadewar da suka yi da ADC a matsayin “mataki na farko.”

Amma hadewar ADC da CNM ba ta yi wani tasiri ba inda ta dore na wata uku kacal.

A watan Agusta 2018, wani bangare na CNM ya fice daga ADC ya kafa sabuwar jam’iyya mai suna New African Democratic Congress (N-ADC).

A watan Yuli 2018, ADC ta shiga kawance da jam’iyyu 36 ciki har da R-APC da PDP don kafa CUPP.

Jam’iyyun sun rattaba hannu kan yarjejeniya domin takarar zaben 2019 karkashin dandalin hadin gwiwa.

Fadar shugaban kasa ta soki masu hadaka

Mun ba ku labarin cewa fadar shugaban kasa ta caccaki masu shirin hadaka domin kwace mulkin Bola Tinubu.

Kara karanta wannan

Zaɓen 2027: Matsalar farko da haɗakar Atiku da ƴan adawa ta fara cin karo da ita

Hadimin Tinubu a bangaren sadarwa, Bayo Onanuga ya ce wasu daga cikin ‘yan ADC na yanzu sun bar APC tun tuni.

Ya zargi Rauf Aregbesola, Hadi Sirika, Abubakar Malami da Rotimi Amaechi da zama marasa biyayya ga APC tun tuni.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.