"Ka Rungumi Ƙaddara, Allah bai Rubuta Za Ka Mulki Najeriya ba," Hadimin Tinubu ga Atiku

"Ka Rungumi Ƙaddara, Allah bai Rubuta Za Ka Mulki Najeriya ba," Hadimin Tinubu ga Atiku

  • Daniel Bwala ya shawarci Atiku Abubakar ya hakura da neman mulki saboda alamu sun nuna ba zai shugabanci Najeriya ba a rayuwarsa
  • Hadimin shugaban ƙasar ya ce Allah ke ba da mulki ga wanda ya so amma ga dukkan alamu Allah ba zai ba Atiku damar shugabancin kasar nan ba
  • Ya buƙaci Atiku ya haɗa kai da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu domin cika burinsa na inganta Najeriya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Mai ba wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu shawara na musamman kan sadarwa, Daniel Bwala ya shawarci Atiku Abubakar ya rungumi ƙaddara.

Bwala ya ce da yiwuwar babu mulkin Najeriya a kaddarar da Allah ya tsarawa tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar a rayuwarsa.

Daniel Bwala tare da Atiku.
Hadimin shugaban kasa, Daniel Bwala ya bukaci Atiku Abubakar ya jingine batun neman mulkin Najeriya Hoto: @BwalaDaniel
Source: Facebook

Hadimin Tinubu ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na TVC a ranar Litinin, 5 ga watan Mayu, 2025.

Kara karanta wannan

Rivers: Komai na iya faruwa da rigima ta kunno kai a kokarin dawo da Fubara

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Daniel Bwala ya tattauna batutuwan da suka shafi mulki da kuma makomar siyasar ƴan adawa a ƙasar nan, kamar yadda The Cable ta tattaro.

Hadimin Tinubu ya ba Atiku shawara

Ya ce lokaci ya yi da Atiku zai rungumi kaddara, ya gane cewa da yiwuwar Allah bai tsara zai shugabanci Najeriya ba a rayuwarsa.

“Idan na samu damar ganinsa ido-da-ido, abin da zan faɗa masa shi ne: ‘Mai girma Alhaji Atiku Abubakar, ka yarda da kaddara."
“Allah ke ba da mulki ga wanda ya ga dama kuma duba da yadda abubuwa ke tafiya, alamu na nuna cewa shugabancin Najeriya ba ya cikin kaddararka.”

- Daniel Bwala.

Bwala ya bukaci Atiku ya haɗe da Tinubu

Ya shawarci Atiku da ya haɗa kai da gwamnatin Tinubu domin bada gudummawa wajen gina ƙasar, koda kuwa hakan zai tabbata ne ta hannun wani.

“Ina ganin akwai hanyoyi da dama da zaka iya bayar da gudummawa. Tun da ka kasance abokin Tinubu tsawon shekaru, ku haɗa kai ku cika burin da kuke da shi na kyautata Najeriya.

Kara karanta wannan

"Ƴan bindiga sun shiga uku": Abin da Tinubu ya ce kan matsalar tsaro a Katsina

“Idan ka yarda da hakan, to za ka bar abin da za a tuna da kai a ƙarshen siyasarka, za ka cika wani ɓangare na burinka, ko da ta hannun abokinka ne.”
Shugaba Tinubu da Atiku.
Daniel Bwala ya shawarci Atiku ya haɗa kai da Bola Tinubu Hoto: @aonanuga1956, @Atiku
Source: Facebook

Matasa sun fara barin jikin Atiku

Amma ya ja hankalin Atiku da cewa, idan ya nace kan takarar shugaban ƙasa, to da yiwuwar ƙarshen siyaarsa ba za ta yi kyau ba.

“Yanzu haka, daga cikin mutanensa na siyasa, ya riga ya rasa kaso mai yawa, watakila kashi 60 zuwa 70 cikin 100, in ji shi.”

Bwala ya bayyana cewa matasan 'yan siyasa da suka yi wa Atiku aiki a baya, yanzu suna neman mulki da kansu kuma ba su da niyyar ja da baya.

Hakeem Baba-Ahmed ya shawarci Atiku

A wani labarin, kun ji cewa tsohon hadimin mataimakin shugaban ƙasa, Dr. Hakeem Baba-Ahmed ya buƙaci Atiku Abubakar ya haƙura da neman zama shugaban Najeriya.

A kwanakin baya ne Hakeem Baba Ahmed ya yi murabus daga kujerar mai ba mataimakin shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa.

A cewarsa, ya kamata Atiku, wanda ya tsaya takara har sau shida a tarihi ya matsa gefe ya ba matasa dama, ya cire burin zama shugaban kasa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262