Ana Raɗe Raɗin Gwamna Zai Koma APC, Ƴan Majalisa 2 Sun Sauya Sheƙa zuwa PDP

Ana Raɗe Raɗin Gwamna Zai Koma APC, Ƴan Majalisa 2 Sun Sauya Sheƙa zuwa PDP

  • Jam'iyyar PDP ta ƙara samun ƙaruwa a jihar Enugu ƙasa da awanni 24 bayan ɗan Majalisar Tarayya, Hon. Dennis Agbo ya fice daga LP
  • Wasu ƴan majalisa biyu, Hon. Mark Chidi Obetta da Hon. Malachi Okey Onyechi sun sauya sheƙa zuwa jam'iyyar PDP mai mulkin jihar
  • Shugaban PDP ya karɓe su hannu bibbiyu, inda aka ji yana cewa akwai ƙarin jiga-jigan siyasa da za su rungumi laima nan ba da jimawa ba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Enugu - Kasa da awanni 24 bayan Hon. Dennis Agbo, ɗan majalisar wakilai, ya fice daga jam’iyyar LP zuwa PDP, wasu ‘yan majalisa biyu sun bi sahunsa.

Waɗanda suka koma PDP sun haɗa da mamba mai wakiltar mazaɓar Nsuƙka/Igbo-Eze ta Kudu a Majalisar Wakilan Tarayya, Hon. Mark Chidi Obetta.

Yan Majalisa 2.
Yan majalisa 2 sun fice da LP zuwa jam'iyyar PDP a jihar Enugu Hoto: Ifeanyi Ogenyi
Source: Facebook

Sai kuma Hon. Malachi Okey Onyechi, ɗan majalisar dokokin jihar Enugu mai wakiltar Nsukka ta Yamma, kamar yadda Punch ta rahoto.

Kara karanta wannan

Saƙon APC ga gwamnan PDP bayan ya fara shinshinar shiga jam'iyyar

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

PDP ta karbi ƴan Majalisa 3 a hukumance

Jaridar Leadership ta tattaro cewa an karɓi ‘yan majalisar guda uku a hukumance a hedkwatar PDP da ke Unguwar GRA a jihar Enugu.

Ficewarsu ta biyo bayan sauya sheƙar ɗan takarar gwamna na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Barista Chijioke Edeoga, wanda ya tattara ya koma PDP.

Edeoga ya yabawa Gwamna Peter Mbah bisa ɗumbin ayyukan ci gaba da yake gudanarwa tare da alƙawarin tallafa wa PDP a jihar.

Yadda jiga-jigan siyasa ke shiga PDP

Tun farko jagora a kwamitin yakin neman zaɓen shugaban ƙasa na LP a Jihar Enugu a 2023, Prince Emeka Mamah, ya sauya sheƙa zuwa PDP.

Mamah ya bayyana cewa kyakkyawan shugabancin Gwamna Mbah ne ya ja shi zuwa jam’iyyar PDP mai mulki a Enugu.

Haka kuma, tsohon sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar LP a jihar da kuma ɗan takarar kujerar shugaban ƙaramar hukumar Igboeze ta Arewa, Barista Titus Odo, ya bi sahunsu zuwa PDP.

Kara karanta wannan

Ayyukan gwamna sun ja ra'ayin Ɗan Majalisar Tarayya, ya sauya sheƙa zuwa PDP

PDP ta ce duk aikin Gwamna Mbah ne

Da yake maraba da sababbin masu sauya shekar, shugaban PDP a Enugu, Dr. Martin Chukwuweike, ya yi ikirarin cewa jam'iyyun adawa a Enugu na rushewa a hankali a hankali.

Ya ce ayyukan alherin da Gwamna Mbah ke zuba wa al'umma ya sa PDP ta ƙara ƙarfi, yayin da manyan jam'iyyun adawa, APC da LP suka kama hanyar mutuwa a jihar.

Gwamna Peter Mbah.
PDP ta kara karfi a Enugu duk da Gwamna Peter Mbah na cikin waɗanda ake raɗe-raɗin za su koma APC Hoto: Peter Mbah
Source: Twitter

Chukwuweike ya ƙara da cewa PDP za ta ci gaba da karɓar ‘yan siyasa masu ƙima daga sauran jam’iyyu, yana mai cewa wasu ƙarin jiga-jigai na dab da shigowa jam'iyyar.

“Ina jin daɗin yadda abubuwa ke tafiya daidai da yadda gwamnanmu ke so. Shi ne ya tsara komai, mu namu aiwatarwa," in ji shi.

Tsohon shugaban APC ya bar jam'iyyar

A wani labarin, kun ji cewa tsohon shugaban APC reshen jihar Enugu, Dr. Ben Nwoye ya yi murabus daga matsayin da mamban jam'iyyar.

Dr. Nwoye ya bayyaja cewa ya yanke shawarar ficewa daga APC ne bayan ya tattauna da magoya baya da abokanansa na siyasa.

Ya kuma soki shugabannin APC na shiyyar Kudu maso Yammacin Najeriya, yana mai cewa ga su da burin kara faɗaɗa jam'iyyar.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262