'Za Mu Hana Mutfwang Tazarce': Minista Ya Fadi yadda APC Za Ta Kwace Filato a 2027

'Za Mu Hana Mutfwang Tazarce': Minista Ya Fadi yadda APC Za Ta Kwace Filato a 2027

  • Ministan jin-ƙai, Nentawe Yilwatda, ya bayyana cewa PDP ba za ta iya ci gaba da mulki a Filato ba, don haka APC za ta karɓi mulki a 2027
  • Farfesan wanda ya kasance ɗan takarar gwamnan APC a zaɓen da ya gabata, ya ce APC ta shirya kwace mulki daga hannun Caleb Mutfwang
  • Ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu zai yi nasara a zaɓen 2027, ya na mai cewa gwamnatinsa ta samar da tsaro a jihar Filato da kewaye
  • Ministan ya ce zai dawo Filato don yi nemawa Tinubu kuri'u a 2027, ya tabbatar da cewa APC za ta yi nasara a jihar ba tare da kalubale ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Filato - Ministan harkokin jin-ƙai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya bayyana cewa jam’iyyar PDP ba za ta iya samun tazarce a jihar Filato a babban zaɓen 2027 ba.

Kara karanta wannan

An ba Kwankwaso shawara kan shirin haɗakar Atiku, Peter Obi da El Rufai a 2027

Yayin da ya buga kirji da cewa APC za ta kwace mulki daga hannun Gwamna Caleb Mutfwang, Nentawe ya kuma ce Shugaba Bola Tinubu zai sake lashe zaɓe a 2027.

Nentawe Yilwatda ya yi magana kan shirin APC na kwace jihar Filato daga PDP a 2027
Ministan jin-kai, Nentawe Yilwatda ya jaddada shirin APC na kwace Filato a zaben 2027. Hoto: @nentawe1
Asali: Twitter

2027: APC za ta karbe mulkin Filato daga PDP

Farfesan Yilwatda, wanda ya kasance ɗan takarar gwamnan Filato na jam’iyyar APC a zaɓen da ya gabata, ya ce jam’iyyarsu ta shirya karɓe mulki, inji rahoton Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ministan ya yi wannan furuci ne yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan rediyon Rhythm FM da ke Jos, babban birnin jihar, a ƙarshen makon nan.

“Babu wani ci gaba na a-zo-a-gani da gwamnatin PDP ta samar a jihar Filato. APC jam’iyya ce mai tausayin jama’a. Mu masu aiki da fada da cikawa ne, ba hayaniyar siyasa ba."

- Prof. Yilwatda.

"Tinubu zai lashe zaben Filato a 2027" - Minista

Ya ƙara da cewa zai dawo Filato lokacin yaƙin neman zaɓe, inda zai yi aiki tukuru domin ganin Shugaba Tinubu ya samu nasara a jihar.

Kara karanta wannan

Fubara: Gwamnonin PDP sun nufi kotun koli kan dokar ta baci a jihar Ribas

“Zan dawo Filato a lokacin yaƙin neman zaɓe. Zan yi wa Tinubu kamfen a 2027, kuma zai yi nasara a jihar Filato,” inji Nentawe Yilwatda.

Ministan ya jaddada cewa ko da yake Filato ba ta zaɓi Tinubu a 2023 ba, amma shugaban ƙasar ya yi kokari sosai wajen daƙile matsalar tsaro a yankin.

Yayin da ya ce yanzu manoma da dama sun fara komawa gonakinsu bayan dogon lokaci na fargaba, Yilwatda ya ce:

“Da irin ci gaban da aka samu a harkar tsaro, Shugaba Tinubu zai lashe jihar Filato a 2027, kuma za jajirce don tabbatar da hakan."

Shirin APC a zaben 2027 a Filato

A yayin da babban zaɓen 2027 ke kara kusantowa, jam’iyyar APC a jihar Filato ta fara shirin karɓe mulki daga hannun PDP, inda manyan shugabanninta ke bayyana kwarin gwiwa kan nasararta.

Ministan jin-ƙai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya tabbatar da cewa jam’iyyarsu za ta yi nasara dumu-dumu a Filato, tare da nuna cewa gwamnatin PDP mai ci ba ta kawo wani gagarumin ci gaba ba a jihar.

Kara karanta wannan

Kwana 1 da dakatar da Fubara, Gwamna ya yi wa Tinubu alkawari kan zaben 2027

Masu fashin baki kan siyasa sun bayyana cewa wannan furuci na Nentawe Yilwatda wata alama ce da ke nuna yadda APC ke ƙara samun kwarin gwiwa a siyasance, musamman ganin cewa ministan ya kasance ɗan takarar gwamna na jam’iyyar a 2023.

Wasu na ganin cewa kasancewarsa a cikin gwamnatin Shugaba Tinubu zai ba shi damar samun goyon baya daga matakin tarayya don cimma burin APC a Filato.

A gefe guda, jam’iyyar PDP a jihar na fuskantar ƙalubale daga ‘yan adawa masu ra’ayin cewa gwamnatinta ba ta yi wani aiki na a-zo-a-gani ba tun bayan hawanta mulki.

Wasu jiga-jigan jam’iyyar APC sun bayyana cewa idan har PDP ba ta sauya salon mulkinta ba, to tabbas za ta fuskanci babban kalubale daga APC a 2027.

Ana so Tinubu ya ayyana dokar ta baci a Osun

A wani labarin, mun ruwaito cewa, tsohon minista, Oyewale Adesiyan, ya nemi ayyana dokar ta-baci a Osun saboda tabarbarewar tsaro da rikice-rikicen siyasa a jihar.

Kara karanta wannan

Bayan shekara 2, Buba Galadima ya fadi wanda ya yi nasara a zaben Legas

Ya zargi Gwamna Ademola Adeleke da kin bin hukuncin kotu, yana mai cewa hakan ne ya haddasa rikicin kananan hukumomi da kuma asarar rayuka.

Adesiyan ya bukaci a yi amfani da sashe na 305 na kundin tsarin mulki domin tabbatar da doka da oda tare da dawo da zaman lafiya a Osun.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng