Manyan Abubuwan Magana 10 da Suka Faru a Majalisar Tarayya Daga 2023 Zuwa 2024

Manyan Abubuwan Magana 10 da Suka Faru a Majalisar Tarayya Daga 2023 Zuwa 2024

Daga lokacin da aka rantsar da majalisar tarayya ta goma, abubuwa da-dama sun faru a cikin shekara guda kenan.

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Sanata Godswill Akpabio da Rt. Hon. Tajuddeen Abbas su ke rike da shugabancin majalisar dattawa da wakilai.

Majalisa
Majalisar tarayya ta goma a bakin aiki a Abuja Hoto: @HouseNgr/@NgrSenate
Asali: Twitter

Abubuwan da suka faru a Majalisa

Daily Trust ta dauko manyan abubuwan da suka jawo surutu a majalisar daga lokacin da aka rantsar da ita a Yunin 2023.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Sabon taken Najeriya

A gurguje ‘yan majalisar tarayya suka amince da sabon taken Najeriya wanda ya sa aka rabu da Arise O Compatriots zuwa We Hail Thee.

Kara karanta wannan

Dangote, Elumelu sun samu shiga yayin da Tinubu ya rantsar da kwamitin tattalin arziki

2. Motocin ‘yan majalisa

Legit ta kawo maku rahotannin yadda gwamnatin Najeriya ta kashe fiye da N50bn domin sayawa ‘yan majalisa motocin hawa kirar SUV.

3. Wa’adin shugaban kasa

Wasu ‘yan majalisa 35 sun kawo kudirin da zai ba shugaban kasa dama yin wa’adi guda rak na tsawon shekaru shida a kan karagar mulki.

4. Komawa mulkin Firayim Minista

Hon. Abdulsamad Dasuki da wasu abokan aikinsa sun kawo shawarar a komawa salon shugabancin Firayim Minista da aka bari a 1966.

5. Binance da zargin 'yan majalisa da rashawa

Kwanaki New York Times ta rahoto shugaban kamfanin Binance, Richard Teng yana cewa ‘yan majalisa sun nemi cin hanci a hannunsu.

6. Kudirin hana gantalin dabbobi

Sanata Titus Tartenger Zam ya kawo kudirin da zai ba da damar kafa wurin kiwon dabbobi, hakan zai hana makiyaya gantali a jihohi.

7. Aikawa ‘yan majalisa kudi

Ana shirin tafiya hutu ne aka ji Godswill Akpabio ya yi subutar baki, ya shaidawa ‘yan majalisa an aiko masu kudin da za su shakata.

Kara karanta wannan

Borno: Majalisar dattawa ta faɗi sakacin da ya jawo aka kai harin bam a Gwoza

8. Binciken badakalar daukar aiki

Kwamitin Hon. Yusuf Adamu Gagdi ya binciki zargin badakala wajen daukar aiki a hukumomi da ma’aikatu, wannan ya jawo yamutsi.

9. Zargin badakalar N3.7tr a kasafin kudi

Sanata Abdul Ningi ya yi zargin cewa akwai N3.7tr da ke cikin kasafin kudi da ba a ware su ga wasu kwangiloli ba, hakan ya tada kura.

10. Dakatar da Abdul Ningi

A dalilin fitowa yana zargin badakala a kasafin kudin shekarar 2024, majalisar dattawa ta dakatar da Abdul Ningi na tsawon watanni uku.

Yadda majalisa ta yaki tazarcen Obasanjo

Ana da labarin cewa tsohon shugaban majalisar dattawa ya tona yadda aka so ba shi cin hanci domin tazarcen Olusegun Obasanjo.

Sanata Adolphus Wabara ya bayyana adadin kudin da aka tura masa har gida domin yarda kudirin a lokacin, amma ya ki yarda.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng