Kano: NNPP Ta Gano Makarkashiyar APC Domin Hana Mulkin Gwamna Abba Samun Nasara

Kano: NNPP Ta Gano Makarkashiyar APC Domin Hana Mulkin Gwamna Abba Samun Nasara

  • Yayin da ake cikin rigimar sarautar Kano, jam'iyyar NNPP ta bayyana waɗanda ke neman ruguza jihar Kano a Arewacin Najeriya
  • Jam'iyyar ta zargi APC da neman kawo rudani a jihar domin kwace mulkin jihar karfi da yaji kuma ta kowace hanya
  • Wannan na zuwa ne yayin da ake zargin Gwamnatin Tarayya da shiga rigimar jihar wajen amfani da bangaren shari'ar da jami'an tsaro

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Jam'iyyar NNPP a Najeriya ta zargi APC da neman kawo rudani a jihar Kano.

Jam'iyyar ta zargi APC mai mulki da neman kwace mulkin Abba Kabir a jihar Kano ta kowace hanya wajen kawo rudani.

Kara karanta wannan

Sarautar Kano: Lauyoyin Arewa sun yabawa hukuncin kotu, sun gargaɗi gwamna Abba

Jam'iyyar NNPP ta zargi APC da kawo rudani a Kano
Jami'yyar NNPP ta zargi APC da neman kwace mulkin Abba Kabir a Kano. Hoto: Abba Kabir Yusuf, Dr. Abdullahi Ganduje.
Asali: Facebook

NNPP ta zargi APC a rigimar Kano

Wannan na kunshe ne a cikin hirar da kakakin jam'iyyar ta kasa, Ladipo Johnson ya yi da Plus TV a ranar Laraba 19 ga watan Yunin 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Johnson ya ce APC na neman kifar da gwamnatin Abba Kabir Yusuf karfi da yaji wajen kawo rudani a jihar, cewar Vanguard.

Ya ce yadda APC ta yi kane-kane a rigimar sarautar Kano hakan ya nuna damuwarta wurin kwace mulkin Kano ta kowace hanya.

"APC ba su taba boye maitarsu ta neman rikita Kano da kwace ikon halastaccen Gwamna Abba Kabir ba."

- Ladipo Johnson

NNPP ta shawarci ƴan Najeriya kan APC

Jami'yyar NNPP ta ce APC na amfani da bangaren shari'a da kuma jami'an tsaro domin kawo rudani a jihar.

Ta bukaci ƴan Najeriya da su tashi tsaye kan wannan makirci da APC ke ƙullawa da ba zai haifar da ɗa mai ido ba.

Kara karanta wannan

Kungiyar Arewa ta yi matsaya bayan shari'ar Kano, ta gargadi Abba kan tayar da fitina

Kwankwaso ya zargi Tinubu kan rigimar Kano

A wani labarin mai kama da wannan, Sanata Rabiu Kwankwaso ya zargi Gwamnatin Tarayya kan rigimar sarautar Kano.

Kwankwaso ya ce Bola Tinubu yana kokarin kawo rudani a jihar domin sanya dokar ta ɓaci da kwace mulkin Kano.

Daga bisani, Bola Tinubu ya musanta zargin da Kwankwaso ya ke yi kan gwamnatinsa inda ya ce babu kamshin gaskiya a maganar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.