Barau, Ndume da Sauran Sanatoci da Ka Iya Rasa Kujerunsu Kan Babban Kuskure

Barau, Ndume da Sauran Sanatoci da Ka Iya Rasa Kujerunsu Kan Babban Kuskure

  • Kungiyar ALDRAP ta maka wasu mambobin Majalisar Dattawa kusan 40 a gaban babbar kotun Tarayya da ke Abuja
  • Kungiyar ta na kalubantar sanatocin ne kan rike mukamai a mabambantan Majalisu da suka hada da na ECOWAS da Pan-African
  • Daga cikin wadanda suka shiga matsala akwai mataimakin shugaban Majalisar, Barau Jibrin da Ali Ndume da Smart Adeyemi da sauransu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Mambobin Majalisar Dattawa akalla 40 ne ka iya rasa kujerunsu ciki har da mataimakin shugaban Majalisar, Sanata Barau Jibrin.

Duk da kasancewarsu a Majalisar Tarayyar Najeria suna kuma da rike da kujeru a Majalisar ECOWAS da kuma ta Pan-African.

Kara karanta wannan

Ba a gama da dambarwar Ganduje ba, an sake korar shugaban APC a Zamfara

Barau da sanatoci 40 za su iya rasa kujerunsu a Majalisa
Sanata Barau da Ndume ka iya rasa kujerunsu kan kasancewa a majalisu 2. Hoto: @adamugarba.
Asali: Twitter

Sanatocin da ka iya rasa kujerunsu

Bayan sanata Barau wanda shi ne ke rike da mukamin mukaddashin shugaban Majalisar akwai sanata Ali Ndume, cewar Premium Times.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sauran sun hada da Smart Adeyemi da Mshelia Haruna da Abiodun Olujimi da Tolu Odebiyi da sauransu.

Wannan na zuwa ne bayan maka 'yan majalisun a Babbar Kotun Tarayyar da cibiyar ALDRAP ta yi.

ALDRAP na neman tabbatar da gaskiya da bin diddigi kan dukkan al'amuran shugabanci ba tare da kwana-kwana ba.

Sakon kungiyar ga Akpabio kan sanatocin

Kungiyar ta bukaci shugaban Majalisar, Godswill Akpabio ya rusa kujerunsu saboda rike mukamai a mabanbantan Majalisu tare da karbar alawus.

Bayan Akpabio ya gagara daukar wani mataki kan wannan lamari, kungiyar ta dauki matakin shiga kotu.

Kungiyar ta yi barazanar a cikin wata takarda da sakatarenta, Tonye Clinton Jaja ya sanyawa hannu a ranar 8 ga watan Afrilun wannan shekara.

Kara karanta wannan

Kudurin Majalisa: Za a rika yankewa masu safarar miyagun kwayoyi hukuncin kisa

Har ila yau, kungiyar ta ce kasancewarsu a majalisu biyu ya saba doka sashe na 68 na kundin tsarin mulkin 1999.

Majalisa ta dauki mataki kan safarar kwayoyi

A wani labarin, Majalisar Tarayya ta amince da dokar hukuncin kisa kan masu safarar kwayoyi a fadin ƙasar.

Majalisar ta amince da hakan ne bayan kai ruwa rana game da matakin yayin zaman Majalisar tsakanin mambobinta.

Sanata Adams Oshiomole ya kalubalanci dokar inda ya ce ba a gaggawa kan irin wannan da ya shafi rai da rayuwar ɗan Adam.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.