Gwamnan APC Ya Gana da Tinubu Kan Muhimmin Batu da Ya Shafi Tsaro a Jihar Arewa
- Gwamna Ahmed Ododo na jihar Kogi ya ziyarci shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu kan batun tsaro ranar Laraba da ta gabata
- A wata sanarwa da kakakin gwamnan ya fitar, ya ce Ododo ya yi wa Tinubu bayanin halin da ake ciki a jihar Kogi
- Shugaba Tinubu ya jinjinawa gwamnan bisa yadda ya fara mulki da ƙafar dama, inda ya tabbatar masa da cewa zai mara masa baya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
FCT, Abuja - Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Ododo ya kai ziyara ta musamman ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnati da ke birnin tarayya Abuja.
Yayin wannan ziyara, Gwamna Ododo ya tattauna da Shugaba Tinubu kan sha'anin tsaro a jihar Kogi da ke Arewa ta Tsakiya a Najeriya.

Kara karanta wannan
Okuama: Bola Tinubu ya gana da gwamnan PDP kan kisan sojoji 17, sahihan bayanai sun fito

Source: Twitter
Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Ismaila Isah, ya fitar, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Abin da Ododo ya faɗawa Tinubu
Ya ce gwamnan ya faɗawa shugaba Tinubu halin da ake ciki game da tsaro a jihar Kogi, gami da kokarin da gwamnatinsa ke yi na inganta tsare-tsaren samar da tsaro mai ɗorewa.
Gwamnan ya kuma yabawa shugaba Tinubu kan kokarinsa na ganin an gaggauta daukar matakin magance kalubalen ƙarancin abinci a kasar nan.
Sannan ya sanar da shugaban kasar irin kalaman yabon da suka fito daga al'ummar jihar Kogi biyo bayan rabon tallafin kayan abinci a jihar a watan jiya.
Gwamna Ododo ya kuma tabbatar da kudirinsa na samar da abinci a jihar Kogi ta hanyar tsaftace gonaki da tallafawa manoma domin bunƙasa harkokin noma da sarrafa kayan abinci.

Kara karanta wannan
Kano: Gwamna Abba Kabir ya ware maƙudan kuɗi domin ciyar da mabuƙata a watan Ramadan
Ya kuma yabawa shugaba Tinubu kan hanzari da jajircewar ma’aikatar ayyuka ta ƙasa wajen ganin an kammala ayyukan titunan gwamnatin tarayya a kan lokaci a jihar Kogi.
Tinubu ya jinjinawa sabon gwamnan
A nasa jawabin, shugaba Tinubu ya yabawa Gwamna Ododo bisa yadda ya fara taka rawar gani a matsayin gwamnan jihar Kogi, kamar yadda Tribune ta rahoto.
Ya kuma ba shi tabbacin cewa gwamnatin tarayya karkashin jagorancinsa za ta ci gaba da mara masa baya a kokarinsa na kawo sauyi a jihar.
Gwamna Radɗa ya tallafawa mata a Katsina
A wani rahoton kuma Malam Dikko Radda ya rabawa mata da ƴan matan da hare-haren bindiga ya shafa tallafin N150,000 domin su fara sana'a.
Gwamnan Katsina ya kuma raba tallafin N100,000 ga iyaye mata da ƴan matan da cutar korona ta durkusar da kasuwancinsu a kananan hukumomi 34 na Katsina.
Asali: Legit.ng