Sabon Rikici Zai Kurdo Jam’iyyar PDP, Atiku Ya Lula Zuwa Dubai Bayan Shari’ar Zabe

Sabon Rikici Zai Kurdo Jam’iyyar PDP, Atiku Ya Lula Zuwa Dubai Bayan Shari’ar Zabe

  • Sule Lamido ya yi Allah-wadai da yadda abubuwa su ke tafiya a jam’iyyarsa ta PDP a karkashin jagorancin ‘yan NWC
  • A ra’ayin tsohon gwamnan Jigawa, sakacin shugabannin jam’iyyar PDP ya jawo Bola Tinubu yana katsalandan a Ribas
  • Idan za a bi ta Sule, akwai bukatar Iliasu Damagum da mutanensa su sauka daga mukaman da su ke kai a halin yanzu

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Jigawa - Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya fito ya fara maganganu game da halin da jam’iyyar PDP ta ke ciki a yau.

Alhaji Sule Lamido ya bukaci shugabannin jam’iyyarsu ta PDP na matakin kasa su sauka daga kujerunsu, ya yi kiran ne a Facebook.

Kara karanta wannan

Nazarin Shekarar 2023: Peter Obi, Kwankwaso da ‘Yan siyasa 6 da suka fi kowa tasiri a shekarar 2023

Jam’iyyar PDP
Jagororin Jam’iyyar PDP Hoto: @Atiku @GovWike
Asali: Twitter

Sule ya soki PDP NWC a kan rikicin Ribas

‘Dan siyasar ya nuna idan har PDP ba za ta iya kare Siminalayi Fubara a rikicinsa da Nyesom Wike ba, majalisar NWC ta gaza aikinta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A wani dogon jawabi da ya yi a shafinsa a dandalin na Facebook a ranar Laraba, ya ce bai kamata a zura ido a rikicin jihar Ribas ba.

Tsohon Ministan harkokin wajen kasar ya ba Gwamna Simi Fubara shawara ya yi watsi da yarjejeniyar da aka dauka a Aso Villa.

"Shin PDP ta na da kwamitin gudanarwa na kasa, ko kuwa dai a ce muna da wata jam’iyya mai suna PDP har yanzu?
Idan muna da daya daga cikin biyu, ta ya ba su nan a abin da yake faruwa da ‘ya ‘yan jam’iyyar PDP a Ribas?"

- Sule Lamido

Kara karanta wannan

Atiku, Amaechi, Shekarau, Binani da jiga-jigan ‘yan siyasa da suka fi kowa asara a 2023

Sule wanda yana cikin kwamitin amintattu ya ce abin kunya ne yadda aka bari shugaban kasa ya tsoma masu baki a jihar Ribas.

Matashi 'dan PDP ya ce a kori NWC

Adnan Mukhtar Tudun Wada wanda matashin ‘dan jam’iyyar PDP ne a reshen Kano ya ce shakka babu akwai bukatar ta sake zani.

Malam Adnan Tudun Wada yana cikin masu goyon bayan Iliasu Damagum su yi waje, ya fadawa Legit wannan a safiyar Juma’a.

‘Dan siyasar ya zargi Damagum da majalisarsa da yi wa Nyesom Wike aiki, yake cewa ba su dace a bar jam’iyya a hannunsu ba.

"Ya kamata a kira karamin gangami, su canza Damagum da wanda ya cancanta ya jagoranci ja’iyyar nan yadda ya dace."

- Adnan Mukhtar Tudun Wada

PDP: Ina Atiku Abubakar?

A duk abubuwan nan da ke faruwa, Legit ta na zargin Alhaji Atiku Abubakar wanda shi ne jagoran jam’iyyar adawar yana kasar waje.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu da wasu jiga-jigai na cikin matsala, Shugaban PDP na ƙasa ya ɗau zafi

Dino Melaye ya fito da wasu hotuna da ke nuna ‘dan takaran na PDP ya tafi birnin Dubai.

Asali: Legit.ng

Online view pixel