Kano: Ana Son Hukunta Abba Ne Don 2027, Masu Zanga-zanga a Abuja Sun Fusata, Sun Ba da Misali

Kano: Ana Son Hukunta Abba Ne Don 2027, Masu Zanga-zanga a Abuja Sun Fusata, Sun Ba da Misali

  • Daruruwan masu zanga-zanga ne su ka cika birnin Abuja don kalubalantar hukuncin shari'ar zaben jihar Kano
  • Masu zanga-zangar sun fito daga ko wane bangare na kasar inda su ka nuna rashin jin dadinsu da abin da aka yi a jihar Kano
  • Wani matashi daga jihar Akwa Ibom ya ce dole ya fito zanga-zangar saboda watarana hakan zai iya faruwa a jiharsa

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Dandazon jama'a na ci gaba da zanga-zanga a birnin Tarayya, Abuja kan hukuncin shari'ar jihar Kano.

Masu zanga-zangar sun kuma nuna rashin jin dadinsu da hukuncin jihohin Zamfara da Plateau har ma da jihar Nasarawa.

Masu zanga-zanga sun cika birnin Abuja, sun nemi a yi wa Abba Kabir adalci
Masu zanga-zanga sun yi Allah wadai da shari'ar zaben Kano. Hoto: Abba Kabir Yusuf.
Asali: Twitter

Wane gargadi masu zanga-zangar su ka yi?

Kara karanta wannan

Maulidi: Atiku ya yi martani kan harin bam da aka yi kan bayin Allah a Kaduna, ya ba da shawara

Har ila yau, sun gargadi mahukunta da su kiyayi kawo cikas a kujerar Abba Kabir na jihar Kano inda su ka bukaci adalci a shari'ar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jama'a da dama na ci gaba da nuna rashin jin dadinsu musamman a hukuncin Kotun Daukaka Kara da aka yi a shari'ar jihar Kano.

Matasan sun bayyana cewa an shirya abin ne don hukunta Abba Kabir shi kadai saboda zaben 2027, cewar Tribune.

Masu zanga-zangar sun hada da mutane daga Arewacin kasar har zuwa Kudancin Najeriya da kuma mazauna yankunan Wasa da Madala a Abuja.

Mafi yawan masu zanga-zangar mata ne da suka bayyana ra'ayinsu da yarukan Hausa da Ibo da Fulani da Yarbanci.

Wane martani masu zanga-zangar ke yi?

Masu zanga-zangar sun yi hakan ne don nuna cewa kansu a hade ya ke don yaki da rashin adalci, cewar Newstral.

Kara karanta wannan

Rikicin siyasar Kano: Laifin wanene? Mai fashin baki ya yi cikakken bayani

Wani daga cikinsu mai suna Ekwerre ya bayyana cewa ya shiga zanga-zangar ce don nuna rashin jin dadin abin da aka aikata a Kano.

Ya ce idan zai faru a Kano to wata rana zai iso jiharsa ta Akwa Ibom da kuma sauran jihohin Najeriya baki daya.

Abba Kabir ya bankado badakalar kayan tallafi

A wani labarin, Gwamna Abba Kabir na jihar Kano ya yi nasarar bankado wata badakala ta kayan tallafin rage radadi.

Wannan na zuwa ne bayan gwamnan ya kaddamar da kayan tallafi a kwanakin baya don tallafa wa marasa karfi a jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.