Gwamnan Arewa Ya Tsorata da Ganin Sabbin Fuskoki a Jihar Yayin da Ake Shirin Yanke Hukuncin Zabe
- Yayin da ake shirin yanke hukuncin shari'ar zaben gwamna a Nasarawa, Gwamna Sule ya fara korafi da zarge-zarge
- Gwamnan ya ce akwai wasu sabbin fuskoki da ke shigo wa jihar musamman a karamar hukumar Keffi da ke jihar
- Wannan na zuwa ne yayin da ake shirye-shiryen yanke hukunci a shari'ar zaben gwamnan jihar a gobe Laraba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Nasarawa - Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya yi korafi kan wasu sabbin fuskoki da ke shigo wa jihar a 'yan kwanakin nan.
Gwamnan ya yi wannan korafi ne yayin da ake shirin yanke hukuncin shari'ar zabensu a gobe Laraba 15 ga watan Nuwamba.

Source: Twitter
Mene Sule ke cewa kan hukuncin kotun?

Kara karanta wannan
Zaben Kogi: INEC ta fitar da sabuwar sanarwa kan sake zabe a jihar Kogi, ta fadi ranar da za a yi
Sule ya ce yawan shigowar mutane baki jihar musamman karamar hukumar Keffi ya fara ta da hankulan mutanen jihar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya kirayi dukkan magoya bayansa da sauran jama'ar jihar da su yi kokarin danne zuciyarsu, Daily Trust ta tattaro.
Idan ba a mantaba, kotun zabe ta kwace kujerar Gwamna Sule na jam'iyyar APC kan wasu kura-kurai da aka samu a zaben gwamnan a jihar.
Wane hukunci karamar kotu ta yanke a baya?
Kotun ta tabbatar da David Ombugadu na jam'iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar, cewar Within Nigeria.
Daga bisani Gwamna Sule ya daukaka kara zuwa kotu don kalubalantar hukuncin karamar kotun da ta yi a Lafia babban birnin jihar.
Kotun daukaka kara ta sanya gobe Laraba 15 ga watan Nuwamba a matsayin ranar yanke hukuncin shari'ar zaben gwamnan jihar a Abuja.
Kotu ta sanya ranar yanke hukuncin zaben Nasarawa
A wani labarin, kotun daukaka kara ta sanya ranar raba gardama a shari'ar da ake yi na zaben gwamnan jihar Nasarawa.

Kara karanta wannan
Zaben Kogi: a karshe, Dino Melaye ya yi martani kan dokuwa da yake a zabe, ya fadi abin da INEC za ta yi
Kotun ta saka Laraba 15 ga watan Nuwamba a matsayin ranar yanke hukuncin shari'ar da ta bai wa Ombugadu na PDP nasara a zaben gwamnan.
Wannan na zuwa ne bayan kotun ta kwace kujerar Gwamna Sule Abdullahi na jam'iyyar APC a hukuncin karamar kotun.
Asali: Legit.ng