"Ni Dalibi Ne Mai Hazaka" Shugaba Tinubu Ya Bayyana Tarihin Karatunsa a Jami'a

"Ni Dalibi Ne Mai Hazaka" Shugaba Tinubu Ya Bayyana Tarihin Karatunsa a Jami'a

  • Shugaba Bola Tinubu ya bayyana tarihinsa na karatu a lokacin da yake jami'a, inda ya ce shi hazikin dalibi ne
  • Yayin da yake jawabi ga ‘yan Najeriya mazauna Indiya, shugaban ya faɗi yadda Deloitte ya horar da shi sannan ya shiga kamfanin Exxon Mobil
  • Tinubu ya je kasar Indiya ne domin halartar taron G-20, kuma ya gana da 'yan Najeriya wanda daliban Najeriya da ke karatu a kasar suka halarta

India - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa yana da kyakkyawan tarihi na hazaƙa a lokacin yana matsayin ɗalibin jami'a a ƙasar Amurka.

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa shugaba Tinubu ya bayyana haka ne yayin ganawarsa da 'yan Najeriya mazauna ƙasar Indiya ranar Alhamis, 7 ga watan Satumba.

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, yayin gana wa da yan Najeriya a Indiya.
"Ni Dalibi Ne Mai Hazaka" Shugaba Tinubu Ya Bayyana Tarihin Karatunsa a Jami'a Hoto: Dada Olusegun
Asali: Twitter

Shugaba Tinubu ya yi jawabi ga 'yan Najeriya a Indiya

Kara karanta wannan

Hukuncin Kotu: An Bayyana Wani Muhimmin Dalili Da Zai Sanya Shugaba Tinubu Ya Cigaba Da Nasara Akan Atiku Da Peter Obi

A ranar Talata, 5 ga watan Satumba, 2023, Bola Tinubu ya bar fadar shugaban ƙasa da ke Abuja zuwa New Delhi a Indiya, inda aka gayyace shi taron shugabannin ƙasashen G-20.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Vanguard ta ce a wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale, ya fitar ya bayyana cewa taron ya samu halartar ɗaliban Najeriya da ke karatu a ƙasar Indiya.

Shugaba Tinubu ya bayyana kwarin guiwar cewa ɗaliban zasu cimma nasara a karatun da suke yi daban-daban idan suka sa gaskiya da sadaukarwa.

Tinubu ya faɗi yadda ya fara aiki da Exxon Mobil

Sanarwan ta tattaro cewa shugaban ƙasa ya yi farin ciki da haɗuwa da 'yan Najeriya mazauna Indiya, inda ya ce iliminsa ne ya kai shi matsayin da ya taka yanzu.

"Na fara da ƙarami, ni mai gadi ne, ina koyar da ɗalibai a makaranta, ni ɗalibi ne mai hazaƙa. Na shiga Deloitte kuma ɗaya daga cikin manyan kamfanonin lissafin kuɗi a duniya ya horar da ni saboda karatuna."

Kara karanta wannan

Atiku Abubakar Ya Taya Shugaba Tinubu Murnar Samun Nasara a Kotu? Gaskiya Ta Bayyana

Tinubu ya ƙara da cewa ya tambayi kamfanin ko suna da rassa a Najeriya, sai suka shaida masa cewa suna da abokan hulda da yawa a kasarsa da za su iya daukarsa aiki.

Daga nan ya bayyana cewa a haka ya shiga kamfanin Exxon Mobil kuma saboda nasarar da ya samu a muƙaman babban Odita Janar, Ma’aji da Akanta.

Gwamnan APC Da Ya Shafe Watanni Yana Jinya a Ƙasar Waje Ya Dawo Najeriya

A wani rahoton na daban Gwamna Rotimi Akeredolu na jihar Ondo ya dawo gida Najeriya daga ƙasar Jamus inda ya shafe dogon lokacin yana jinya.

Gwamna Akeredolu ya bar Najeriya zuwa ƙasar Jamus watanni da dama da suka gabata domin jinyar rashin lafiyar da yake fama da ita.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262