Jerin Sunayen Tsofaffin Gwamnoni 5 Da Suka Shiga Kashi Na Biyu Na Ministocin Tinubu

Jerin Sunayen Tsofaffin Gwamnoni 5 Da Suka Shiga Kashi Na Biyu Na Ministocin Tinubu

Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya aika da kaso na biyu na sunayen mutanen da zai naɗa ministoci zuwa Majalisar Dattawan Najeriya a ranar Laraba 2 ga watan Agusta.

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa Femi Gbajabiamila ne ya mika jerin sunayen ƙarin mutane 19 ga shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da misalin ƙarfe 03:15 na rana, inji rahoton The Punch.

Tsoffin gwamnoni biyar ne suka samu damar shiga cikin kashi na biyu bayan jerin sunayen ministoci 28 na farko da aka fitar kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

Sunayen tsofaffin gwamnoni 5 da suka shiga cikin jerin ministocin Tinubu
Gwamnoni 5 da suka samu damar shiga cikin jerin ministocin Tinubu. Hoto: Simon Bako Lalong/Governor Adegboyega Oyetola/Governor Bello Matawalle
Asali: Facebook

Tsoffin gwamnoni 5 da suka yi nasarar shiga jerin sunayen ministocin Tinubu kashi na biyu

1. Tsohon gwamnan jihar Osun, Adegboyega Oyetola

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kara karanta wannan

Jerin Sunayen Asalin Johohin da Aka Haifi Ƙarin Ministoci 19 da Shugaba Tinubu Ya Miƙa Majalisa

Oyetola dai shi ne tsohon gwamnan jihar Osun, wanda ya yi wa'adinsa daga shekarar 2018 zuwa 2022.

Ya sha kaye ne a yayin da ya sake tsayawa takara a ƙarƙashin jam’iyyar APC a hannun gwamna jihar mai ci a yanzu, Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023 da ya gabata.

2. Tsohon gwamnan jihar Filato, Simon Lalong

Simon Lalong ya yi gwamna na tsawon shekaru takwas a jihar Filato. Ya yi gwamnan jihar Filato ɗin ne daga 2015 zuwa 2023 a ƙarƙashin jam'iyyar APC.

Sai dai Lalong ya gaza kawo kujerar gwamna da ta shugaban ƙasa a jam'iyyar APC a jihar, inda jam'iyyar PDP ta lashe duka zaɓukan da aka yi.

3. Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle

Bello Mattawale ya yi wa'adinsa matsayin gwamnan jihar Zamfara daga shekarar 2019 zuwa 2023.

Kamar Oyetola, Matawalle ya sha kaye a yayin da ya sake tsayawa takara domin wa'adi na biyu, a hannun Gwamna Dauda Lawal na jam'iyyar PDP.

Kara karanta wannan

Sunayen Ministoci: Jerin Iyayen Gida Masu Tasowa a Siyasance Da Ka Iya Zama Ministocin Tinubu

4. Tsohon gwamnan jihar Yobe, Ibrahim Geidam

Ibrahim Geidam tsohon gwamnan jihar Yobe ne da ya shafe shekaru 10 a karagar mulki, wato daga 2009 zuwa 2019.

Ya karbi mulki ne a hannun gwamna Mamman Bello Ali, wanda Allah ya yi wa rasuwa sakamakon ciwon hanta a jihar Florida ta ƙasar Amurka.

A yanzu haka shine Sanata mai wakiltar Yobe ta Gabas a Majalisar Dattawan Najeriya.

5. Tsohon Gwamnan Kebbi, Atiku Bagudu

Atiku Bagudu ya yi gwamnan jihar Kebbi na tsawon shekaru takwas, wato tsakanin watan Mayun 2015, zuwa watan Mayun 2023.

Bagudu ya riƙe kujerar sanata da ke wakiltar Kebbi ta Tsakiya a ƙarƙashin jam'iyyar PDP, daga 2011 zuwa 2015.

Hannatu Musawa ta sharɓi kuka a lokacin da ake tantance ta a Majalisar Dattawa

Legit.ng a baya ta kawo muku rahoto kan kukan da Hannatu Musa Musawa ta sharɓa yayin da ta bayyana a zauren Majalisar Dattawa, domin a tantance ta matsayin minista daga jihar Katsina.

Kara karanta wannan

Emefiele: Peter Obi Ya Dau Zafi Kan Takaddamar Jami'an DSS Da Na Gidan Yari a Kotu, Ya Bayyana Matakin Da Ya Dace a Dauka

Hakan ya faru ne a lokacin da take bayar da tarihin rayuwarta, yadda mahaifinta ya taso a matsayin talaka mai ƙaramin ƙarfi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng