Lagas, Ribas Da Wasu Jihohin Da Jam’iyyar Adawa Bata Taba Mulki a Cikinsu Ba

Lagas, Ribas Da Wasu Jihohin Da Jam’iyyar Adawa Bata Taba Mulki a Cikinsu Ba

A duk shekarar zabe, jam'iyyun siyasa na fita don kwato sabbin jihohi da kuma jajircewa wajen ganin wuraren da suke mulki bai kubce masu ba.

Sai dai kuma, wasu jihohi takwas cikin 36 da ke Najeriya basu jijjiga ba tun 1999, domin dai har yanzu wata jam'iyyar adawa bata taba mulki a cikinsu ba.

Wasu manyan yan siyasar Najeriya
Lagas, Ribas Da Wasu Jihohin Da Jam’iyyar Adawa Bata Taba Mulki a Cikinsu Ba Hoto: Asiwaju Bola Tinubu/ Kashim Shettima/Gov Nyesom Ezenwo Wike - CON/Dr.Ifeanyi Arthur Okowa
Asali: Facebook

Ga jerin jihohin da wata jam'iyyar adawa bata taba mulki a cikinsu ba tun 1999 a kasa:

Jihar Lagas

Tun bayan dawowar damokradiyya a 1999, lokacin da jam'iyyar Alliance for Democracy (AD) ta lashe kujerar gwamna, jihar Lagas bata taba fadawa a hannun yan adawa ba.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Daga AD zuwa jam'iyyar Action Congress of Nigeria (ACN) da All Progressive Congress (APC), jihar dai ta kasance ne a hannayen shugabanni guda.

Kara karanta wannan

Ni ba barawo bane: Sanatan APC ya sharbi kuka a majalisa, ya fadi sharrin da aka masa

AD ta koma ACN a Lagas bayan shugaban kasa Bola Tinubu, wanda ya kasance gwamnan jihar ya bar AD don kafa sabuwar jam’iyya. Jam’iyyar ACN ta yi maja da CPC, ANPP, da sauran jam’iyyun siyasa inda suka kafa APC.

Jihar Delta

Jihar ta kasance a hannun jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) tun 1999. Jam'iyya mai mulki a jihar Delta ta kasance PDP.

Jihar ta kudu maso kudu ta yi gwamnoni hudu dukkansu daga jam'iyya daya.

Jihar Akwa Ibom

Wannan wata jaha ce ta kudu maso kudu da ta ki yarda ta watsar da babbar jam'iyyar adawar kasar, PDP, tsawon shekaru 24 da suka gabata.

Tun daga shekarar 1999 har zuwa 2023, jam'iyyar PDP ce ke rike da kambun shugabanci a jihar Akwa Ibom.

Jihar Ribas

Jihar Ribas na daya daga cikin jihohin da PDP ta yi zaman katutu a kan kujerar gwamna.

Tun 1999 sakamakon zaben guda daya ne inda jam'iyyar PDP ke yin nasara.

Kara karanta wannan

Tsohon Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Sauya Sheka Zuwa Labour Party, Ya Fadi Dalili

Jihar Bayelsa

Saura kadan jihar tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ta rasa matsayinta cikin jerin jihohin da jam'iyyar adawa bata taba mulki a cikinta ba lokacin da Gwamna mai ci Diri ya sha kaye a hannun dan takarar APC. David Lyon a zaben gwamna na Disambar 2019.

Sai dai kuma, nasarar APC ba ta kai ko'ina ba yayin da kotu ta tsige Lyon saboda mataimakinsa Biobarakuma Degi-Eremienyo, ya gabatarwa INEC da bayanan karya.

Jihar Enugu

Jihar Enugu ita ce ta gaba cikin rukunin jihohin da ba a taba samun dan adawa da ya yi shugabanci a cikinta ba. Ita kadai ce jihar kudu maso gabas da ke karkashin PDP kuma ta tsallake guguwar zaben Peter Obi wanda ya share yankin a zaben da ya gabata.

Jihar Borno

Mahaifar mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ta ci gaba da bin tsarin zabe guda cikin shekaru 24 da suka gabata.

Kara karanta wannan

Bayanai Sun Bullo Kan Sa Labulen Tinubu da Gwamnonin da Suka Yaki Atiku a PDP

Da farko jam'iyyar All Peoples Party (APP) wacce ta rikide ta zama All Nigeria Peoples Party (ANPP) sannan ta koma APC ce ke shugabanci a jihar.

Jihar Yobe

Jihar Yobe ita ce ta karshe a wannan rukunin kuma tana kamanceceniya da makwabciyarta ta arewa maso gabas wato Borno.

Yobe tana da irin tsari guda da Borno, tun daga APP, ANPP, zuwa APC a 2015.

Zaman lafiyar Najeriya na gaba da aljihunmu, Shettima ga zababbun sanatoci

A wani labari na daban, Mataimakin shugaban kasa ya ja hankalin zababbun sanatoci gabannin rantsar da majalisa ta 10.

Kashim Shettima ya kalubalanci yan majalisar da kada su yarda su karbi cin hanci wajen zabar shugabanni.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng