Hadiza Bala Usman Ta Rubuta Littafin da Ya Tona Abin da Ya Jawo Amaechi Ya Kore ta a NPA

Hadiza Bala Usman Ta Rubuta Littafin da Ya Tona Abin da Ya Jawo Amaechi Ya Kore ta a NPA

  • Hadiza Bala Usman ta rubuta littafin da ya yi bayani a kan wa’adinta a Hukumar NPA ta kasa
  • ‘Yar siyasar ta ce Ministan sufuri na lokacin, Rotimi Amaechi ya dauki karon tsana ya daura mata
  • A karshe Amaechi ya ga bayan Bala Usman, duk da an yi ta kokarin a lallabi Ministan tarayyar

Abuja - Tsohuwar shugabar NPA ta kasa, Hadiza Bala Usman ta rubuta littafin da ya yi bayani a kan sabanin da aka samu da ita a lokacin ta na ofis.

Premium Times ta ce Hadiza Bala Usman ta zargi Mai gidanta, Rotimi Amaechi da korarta daga ofis saboda ta ki taimaka masa da wasu alfarma.

Bala Usman ta kira littafin da “Stepping on Toes: My Odyssey at the Nigerian Ports Authority”, ma’ana takalmin karfe, labari na a hukumar NPA.

Kara karanta wannan

Fadar Shugaban Kasa Ta Bayyana Koma Bayan da Rashin Lafiyar Shugaba Buhari Ta Jawo a Najeriya

Littafin na Bala Usman ya zargi Ministan sufuri na lokacin watau Rotimi Amaechi da jin haushinta saboda kurum ba tayi masa abin yadda yake so.

Gwamnoni sun nemi su tsoma baki

‘Yar siyasar ta ce Amaechi ya nuna wannan a lokacin da kungiyoyi a jagororin APC suka nemi su tsoma baki a lokacin da aka dakatar da ita daga aiki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tawagar Atiku Bagudu ta kungiyar Gwamnonin APC ta zauna da Ministan kan maganar, ya dage dole sai an bincike ta domin an boye wasu kudi.

Hadiza Bala Usman
Hadiza Bala Usman a NPA Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

"Da Gwamnonin su ka matsa masa, sai ya fada masa yanzu abin ya fi karfin teburinsa, sai su tuntubi shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya.
Ya fadawa wani da ya nemi ya sa baki na cika son-kai, babu alherin da na yi masa a NPA, ban taba ba shi kyautar murnar ranar haihuwarsa ba.

Kara karanta wannan

Dubu ta cika: Yadda dan kasar waje ya shigo Najeriya da kayan hodar iblis a cikin kwaroron roba

- Littafin Hadiza Bala Usman

A cewar Bala Usman, Ministan (na lokacin) ya hakikance a kan dole sai ta bar ofis, ya bukaci tayi murabus ko dai ta kalubalanci matakin a gaban kotu.

"Ba zan yi ritaya ko in je kotu ba" - Hadiza Bala Usman

Daily Nigerian ta ce tsohuwar shugaban ma’aikatar fadar gwamnatin Kaduna ba ta karbi shawarar ba, musamman ganin an kafa kwamitin da zai bincike ta.

Ganin ta ki yarda da hakan, ta na ikirarin kwamitin zai gano ba tayi laifi ba, sai Amaechi ya yi alwashin ba za a kammala binciken ba har zuwa 2022.

Burinsa a lokacin shi ne a kai lokacin da aka buga gangar siyasa, take cewa sai a manta da maganar.

Kwamitoci sun zuke Biliyoyi

Tsakanin 2015 zuwa yanzu, Shugaban Kasa ya rantsar da kwamitocin gwamnati kimanin 40 an ji labari Kwamitocin nan sun ci wa Najeriya N20bn.

Kara karanta wannan

Karfin hali: Yadda makaho ya shige soyayya da tsaleliyar budurwa, ya nemi aurenta

Boss Gida Mustapha da Babachir David Lawal ne suka rike ofishin SGF a shekaru 8 da suka wuce. Wasu su na ganin kwamitocin ba su da wani amfani.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng