Shugaban Kasa: Makarantan Legit.ng Sun Tsaida ‘Dan Takara Tsakanin APC, PDP, NNPP da LP

Shugaban Kasa: Makarantan Legit.ng Sun Tsaida ‘Dan Takara Tsakanin APC, PDP, NNPP da LP

  • Mun tambayi masu karanta labaranmu game da wanda suke so ya zama Shugaban kasar Najeriya
  • Mafi yawan wadanda suka shiga zabenmu sun nuna ba su tare da manyan jam’iyyun APC da PDP
  • ‘Dan takaran LP, Peter Obi ya fi Rabiu Kwankwaso, Atiku Abubakar da Bola Tinubu farin jini a zaben na mu

Abuja - Ganin zaben shugaban kasa ya zo, Legit.ng Hausa ta bude filin jin ra'ayi na musamman domin sanin inda makarantamu suka sa a gaba.

Mun tambayi masu bibiyar shafinmu a Twitter cewa a cikin manyan 'yan takaran shugabancin kasar nan, wane za su zaba a mako mai zuwa.

Mutane 5, 596 suka kada kuri’arsu a wannan zabe da aka shirya wanda aka yi kusan kwana biyu ana fafatawa, a karshe Peter Obi ne ya yi galaba.

Kara karanta wannan

Karya ne: Fadar Shugaban Kasa ta Karyata Zargin El-Rufai da Ganduje

LP ta doke APC, PDP da NNPP

‘Dan takaran jam’iyya mai mulki ta APC watau Asiwaju Bola Tinubu ya zo na hudu a zabenmu, ya samu kuri’u 588 ne da ke wakiltar kashi 10.5%.

Wanda ya zo na uku a zaben shi ne Atiku Abubakar mai neman takara a PDP. Tsohon mataimakin shugaban Najeriyan ya samu kuri’un mutane 856.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Na biyu a zaben da jama’a suka yi shi ne Rabiu Kwankwaso wanda ya tsaya a jam’iyyar NNPP, yana da mutane 1533 watau 27.4% na kuri’un.

Shugaban Kasa
Peter Obi a Owerri Hoto: @PeterObi
Asali: Twitter

Peter Obi mai neman mulki a jam’iyyar LP ya fi kowa kaso mai tsoka a filin zaben da mu ka shirya, mutum 2613 da ke wakiltar 46.7% shi suka zaba.

Ga yadda sakamakon zaben yake a kasa:

  1. Asiwaju Bola Tinubu (APC) - 10.5%
  2. Atiku Abubakar (PDP) - 15.3%
  3. Peter Obi (LP) - 46.7%
  4. Rabi'u Kwankwaso (NNPP) - 27.4%

Kara karanta wannan

2023: 'Yan Najeriya sun gaji da Buhari, matar Atiku ta yi bayanai masu daukar hankali

Amma mafi yawan masu magana musamman daga yankin Arewacin Najeriya sun nuna cewa Rabiu Kwankwaso za su ba kuri’arsu a zaben bana.

Wasu kuma sun nuna cewa Atiku Abubakar shi ne mafita a takarar shugabancin kasar nan.

NNPP tayi babban rashi

A daren yau aka tabbatar da labarin rasuwar Hon. Kamilu Ado Wudil wanda yake takarar 'dan majalisa a mazabar Garko da Wudil a zaben 2023.

‘Dan takaran NNPP a zaben ‘dan majalisar wakilan tarayyar Wudil/Garko ya rasu ne ana kusan saura mako daya ayi zaben da yake hangen nasara.

Asali: Legit.ng

Online view pixel