An Yi Watsi Da Sunan Rarara a Kwamitin Kamfen Din Tinubu

An Yi Watsi Da Sunan Rarara a Kwamitin Kamfen Din Tinubu

  • Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta saki sabbin sunaye na ‘ya’yan kwamitin yakin neman zabenta na shugaban kasa
  • A wannan karon ma wasu jaruman masana’antar shirya fina-finan hausa ta Kannywood sun samu shiga jerin
  • Sai dai kuma, ko sama ko kasa ba a ga sunan shahararran mawaki Daudu Kahutu Rarara ba wanda a da yana cikin kwamitin

Jam’iyyar APC ta saki sabbin sunaye na mambobin kwamitin yakin neman zaben dan takararta na shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, bayan ta yi yan gyare-gyare a wanda ta fitar a baya.

Har yanzu shugaban hukumar tace fina-finai ta jihar Kano, Isma'ila Na'abba Afakalla na nan a matsayin mataimakin darakta a bangaren masu nishadantarwa na kwamitin kuma zai jagorancin yankin arewa maso yamma.

Kara karanta wannan

Sunayen da Aka Kara da Wadanda Aka yi Watsi da su a Kwamitin Neman Takarar Tinubu

Rarara
An Yi Watsi Da Sunan Rarara a Kwamitin Kamfen Din Tinubu Hoto: Daily Trust
Asali: UGC

Jarumi Nuhu Abdullahi na nan a matsayinsa na mataimakin mai kula da jin dadin kwamitin yan wasan. Sani Idris Moda ma yana nan a cikin kwamitin.

Sai dai kuma, a wannan karon, ba a ga sunan shahararren mawakin siyasa, Daudu Kahutu Rarara ba a cikin wanda a da shine ke rike da mukamin jami’in kula da harkokin kwamitin na yan wasa.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Rarara ya saki sabuwar waka inda ya soki Gwamna Abdullahi Ganduje na Kano.

A cikin sabuwar wakar da ya fitar don yi wa Tinubu kamfen, Rarara ya tabbatar da rikicinsa da Ganduje kuma ya bayyana gwamnan a matsayin 'Hankaka', ma'ana mutum mai fuska biyu.

Rarara kuma ya zargi Ganduje da daƙile saka sunansa a kwamitin kamfen din shugaban kasa na APC.

Kara karanta wannan

Yanzun Nan: Jam'iyyar APC Ta Fitar da Sunayen Tawagar Kamfen 2023 Na Karshe, An Samu Sauyi

Kamfen 2023: 'Yan A Mutun APC Na Bin Gida-gida Don Tallata Dan Takararsu Bola Tinubu A Wata Jahar Arewa

A wani labarin, wata kungiyar goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, mai suna Jagaban National Coalition ta fara bi gida-gida tana yi masa kamfen.

Jagoran kungiyar a jihar Plateau, Mista Zakariyau Adigun, ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labaran Najeriya a garin Jos, a ranar Talata, 18 ga watan Oktoba.

Adigun ya ce shirin kungiyar shine sanar da duk wani dan jihar nasarorin Tinubu da kyawawan shirin da yake yiwa kasar, rahoton Vanguard.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng