Jerin yan takarar shugaban kasa na APC 20 da suka siya fom din N100m, jam’iyyar mai mulki ta tara N1.95bn

Jerin yan takarar shugaban kasa na APC 20 da suka siya fom din N100m, jam’iyyar mai mulki ta tara N1.95bn

Ana tururuwan siyan fom din takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) duk da tsawwala farashinsa da aka yi wanda ya kai naira miliyan 100.

Jam’iyyar mai mulki dai ta tsawaita wa’adin siyar da fom dinta yayin da kasuwa ke kara bude mata.

Jerin yan takarar shugaban kasa na APC 20 da suka siya fom din N100m, jam’iyyar mai mulki ta tara N1.95bn
Jerin yan takarar shugaban kasa na APC 20 da suka siya fom din N100m, jam’iyyar mai mulki ta tara N1.95bn Hoto: @realRochas, @Official_ABAT, @MobilePunch, @thecableng
Asali: Twitter

Zuwa yanzu, akalla yan takara 20 ne suka siya fom din. Yayin da yan takara 19 suka biya naira miliyan 100 kowannensu, mace daya a cikinsu, Uju Kennedy, ce ta biya 50% daidai da tsarin jam’iyyar.

Da wannan, APC ta tara kimanin naira biliyan 1.95 daga siyar da fom din shugaban kasa kadai.

Yayin da wasu suka siyi fom din da kudinsu, wasu kamar su gwamnan CBN, Godwin Emefiele da shugaban AfDB, Akinwunmi Adesina, sun samu nasu ne daga wasu kungiyoyi koda dai basu riga sun ayyana kudirinsu ba tukuna.

Kara karanta wannan

Babu abin da zai hana PDP karbe mulkin Najeriya a 2023, In ji Ayu

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kafin wa’adin ya cika, ana sanya ran wasu Karin yan takara za su siya nasu fom din. Sai dai, a halin yanzu, ga jerin yan takarar da suka mallaki fom dinsu.

1. Asiwaju Bola Ahmed Tinubu

2. Gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi

3. Gwamna Dave Umahi na jihar Ebonyi

4. Sanata Rochas Okorocha

5. Karamin ministan ilimi Chukwuemeka Nwajiuba

6. Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo

7. Tsohon shugaban majalisar dattawa Ken Nnamani

8. Ministan kwadago Chris Ngige

9. Gwamna Abubakar Badaru na jihar Jigawa

10. Tsohon kakakin majalisar wakilai Dimeji Bankole

11. Sanata Ajayi Boroffice

12. Sanata Ibikunle Amosun

13. Ministan kimiya da fasaha, Ogbonnaya Onu

14. Gwamnan babban bankin kasa (CBN) Godwin Emefiele (yak i karbar fom din)

Kara karanta wannan

‘Yan Majalisar Kano da Kwamishinan Ganduje, za su bi Kwankwaso zuwa Jam’iyyar NNPP

15. Shugaban AfDB, Akinwumi Adesina

16. Gwamana Kayode Fayemi na jihar Ekiti

17. Ministan sufuri Rotimi Amaechi

18. Misis Uju Kennedy, yar takara mace daya tilo

19. Fasto Tunde Bakare

20. Fasto Nicholas Felix

Kada ku barnata kuri'unku, kawai ku zabe ni – Amaechi ga wakilan APC

A wani labarin, ministan sufuri kuma mai son zama shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Rotimi Amaechi, ya ce zabarsa a matsayin wanda zai rike tutar jam’iyyar ba zai zama asarar kuri’u ba.

Amaechi ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, 8 ga watan Mayu, a yayin da yake zantawa da wakilan jam’iyyar a jihar Edo, jaridar The Cable ta rahoto.

Ya bukaci wakilan da su mayar da hankali wajen zabar dan takarara irinsa wanda ya cancanta domin daga tutar jam’iyyar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng