Da Dumi-Dumi: Ministan Sufuri, Amaechi, ya bayyana sha'awar gaje Buhari a 2023

Da Dumi-Dumi: Ministan Sufuri, Amaechi, ya bayyana sha'awar gaje Buhari a 2023

  • Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya bayyana aniyarsa ta gaje Buhari a zaɓen 2023 dake tafe karkashin APC
  • Tsohon gwamnan jihar Ribas ya ayyana kudirinsa a ranar Asabar a Filin wasa na Adokiye Amiesimaka Stadium dake jihar Ribas
  • Ministan ya kasance a gwamnati a muƙamai daban-daban tun bayan dawowar mulkin demokaraɗiyya a 1999

Rivers - Ministan sufuri na tarayyan Najeriya, Honorabul Rotimi Amaechi, ya ayyana shiga tseren takarar kujerar shugaban ƙasa a zaɓen 2023.

Amaechi, wanda ya jima yana musanta raɗe-raɗin shiga takara, ya tabbatar da kudirinsa a hukumance ranar Asabar, 9 ga watan Afrilu, 2022.

Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi.
Da Dumi-Dumi: Ministan Sufuri, Amaechi, ya bayyana sha'awar gaje Buhari a 2023 Hoto: Rt Hon Chibuike R Amaechi/facebook
Asali: Facebook

Ministan ya rubuta a shafinsa na dandalin sada zumunta Facebook cewa:

"Na tsaya a nan gaba gare ku ne domin na bayyana manufa ta kuma na sanar muku da bukata ta aiki a matsayin shugaban ku na gaba."

Kara karanta wannan

Mutane zasu fara cin ciyawa a Arewa saboda tsananin yunwa, Majalisar dinkin duniya

Tarihin siyasar Amaechi

Amaechi ya kasance a cikin gwamnati a muƙaman siyasa daban-daban tun bayan dawowar mulkin demokaraɗiyya a shekarar 1999.

Ya rike kujerar shugaban majalisar dokokin jihar Ribas na tsawon zango biyu daga 1999-2007, bayan haka ya kwashe shekara 8 a kan kujerar gwamnan Ribas daga 2007-2015.

Haka nan kuma Mista Amaechi na ɗaya daga cikin tsirarun ministocin da shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya zarce da su bayan lashe zaɓe a karo na biyu a 2019.

Babu tantama yana ɗaya daga cikin Ministocin wannan gwamnatin da suka taɓuka abun a yaba, kuma shi ne jagoran yaƙin neman zaɓen Buhari a 2015 da 2019.

Tsohon gwamnan ya zama na farko daga cikin yan majalisar gwamnatin Buhari da ya shiga tseren, wasu na sha'awa amma har yanzun ba su ayyana aniyarsu ba.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Na maida mutum 2,000 sun zama Attajirai a jihata, Gwamnan Arewa dake son gaje Buhari

A wani labarin kuma bayan Tambuwal, Bala Muhammed da Wike, wani gwamnan PDP ayyana aniyar shiga takarar shugaban ƙasa a 2023

Gwamnan Akwa Ibom, Udom Emmanuel, ya amsa kiran yan Najeriya na neman takarar shugaban ƙasa a 2023.

Gwamnan ya ce ya karbi Fam ɗin da wata kungiyar kare hakkin ɗan Adam ta siya masa na sha'awar takara a PDP.

Asali: Legit.ng

Online view pixel