Kisan Matafiya a Plateau, Gwamna Ya ba da Umarni bayan Tsoron Barkewar Rikici

Kisan Matafiya a Plateau, Gwamna Ya ba da Umarni bayan Tsoron Barkewar Rikici

  • Gwamnan Plateau, Caleb Mutfwang, ya umarci hukumomin tsaro su tsananta farautar masu hannu a harin Ratatis da ya kashe aƙalla mutum bakwai.
  • Gwamnan ya ce harin abin takaici ne, yana mai jaddada cewa ya kawo koma baya ga zaman lafiyar da ake samu ta hanyar sulhu.
  • Bayan harin, fargaba ta mamaye Jos yayin da shaguna suka rufe, amma jami’an tsaro sun ƙara yawan sintiri.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Jos, Plateau - Gwamnan Plateau, Caleb Mutfwang, ya nuna damuwa game da harin da aka kai a Plateau wanda ya jawo rasa rayuka.

Gwamnan ya umarci hukumomin tsaro da su ƙara kaimi wajen aiki tare da kama waɗanda ke da hannu a mummunan harin da aka kai al’ummar Ratatis a Dorowa Babuje, Barkin Ladi, wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum bakwai.

Kara karanta wannan

Sarakuna sun shiga uku, gwamna ya yi masu barazanar raba da kujerunsu

Gwamna ya fusata kan hare-hare a Plateau
Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Plateau. Hoto: Caleb Mutfwang.
Source: Facebook

Umarnin Gwamna Caleb ya ba jami'an tsaro

Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne cikin wata sanarwa da Zagazola Makama ta samu wanda kwamishiniyar yada labarai ta Plateau, Joyce Ramnap, ta fitar a Jos.

Mutfwang ya yi Allah-wadai da kisan, yana mai kiran lamarin da “ta’addanci mara dalili” da kuma koma baya ga zaman lafiyar da aka samu ta hanyar tattaunawa da sulhu.

A cewar sanarwar, gwamnati ta karɓi labarin harin da girgiza da baƙin ciki mai tsanani, inda aka tabbatar da mutuwar fararen hula da ba su ji ba su gani ba a ranar Lahadi, 22 ga Fabrairu 2026.

Gwamna Mutfwang ya bayyana cewa waɗanda suka jikkata suna samun kulawa a asibitocin da ke kusa, kuma gwamnati na sa ido kan halin da suke ciki domin tabbatar da ingantacciyar jinya.

Ya kuma ce an kafa rundunar haɗin gwiwa ta bincike da ceto, wadda ta ƙunshi jami’an tsaro da jami’an gwamnati, domin taimaka wa waɗanda abin ya shafa, gano ɓatattun mutane da kuma daidaita al’ummar da abin ya rutsa da su.

Kara karanta wannan

DSS na shirin gayyatar yaran El Rufa'i, matar Dadiyata ta yi magana kan dauke mijinta

Ana fargabar barkwar rikici a Jos bayan hare-hare
Taswirar jihar Plateau da ake yawan samun hare-haren yan bindiga da kabilanci. Hoto: Legit.
Source: Original

Gwamna Mutfwang ya tura sakon ta'aziyya

Gwamnan ya miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu, tare da addu’ar samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata, cewar Punch.

Haka kuma ya umarci hukumomin tsaro da su ƙara tsaro a yankin da abin ya shafa da maƙwabta domin hana sake faruwar rikici.

Ya bukaci mazauna yankin su kasance cikin natsuwa, su kiyaye doka, tare da ba da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin taimaka wa binciken da ake yi.

Sai dai sanarwar ba ta ambaci rahotannin mutuwar wasu Fulani a wasu hare-hare dabam ba, ko kuma kisan wasu mutane huɗu da aka ce an kai musu hari bayan zanga-zangar wasu mazauna yankin.

Wannan gibi ya jawo damuwa daga wasu masu ruwa da tsaki, waɗanda ke cewa duk wanda rikicin ya shafa, ba tare da la’akari da ƙabila ba, ya cancanci a ambace shi tare da tabbatar da adalci.

A halin yanzu, fargaba ta mamaye wasu sassan Jos, Jos, inda shaguna da harkokin kasuwanci da dama suka rufe da safiyar Talata, yayin da jami’an tsaro suka ƙara yawan sintiri a wurare masu muhimmanci domin hana ƙarin rikici.

Kara karanta wannan

Gwamna ya fusata da rigimar APC ta lakume rayukan mutane 2, ya ba da umarni

Yan bindiga sun kashe mutan a Plateau

Kun ji cewa wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun kashe Fulani makiyaya tare da sare kan daya daga cikinsu a hanyarsu ta komawa gida.

Kungiyar Miyetti Allah ta yi zargin cewa 'yan kabilar Berom ne suka kai harin, yayin da su kuma matasan Berom suka musanta zargin.

Rundunar soji ta 'Operation Enduring Peace' ta tabbatar da faruwar lamarin sannan ta bayyana matakan da ta dauka zuwa yanzu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.