Tankar Mai Ta Kutsa cikin Ayarin Motocin Shugaban Majalisa, Akpabio, an Rasa Rai

Tankar Mai Ta Kutsa cikin Ayarin Motocin Shugaban Majalisa, Akpabio, an Rasa Rai

  • An samu rasa rai bayan wata tankar mai ta buge ayarin motocin Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio
  • Majiyoyi sun tabbatar da cewa lamarin ya yi ajalin kashe wani jami’in da ke tare da su mai suna Ibrahim Hussaini
  • Akpabio ya bayyana cewa marigayin ya bar mata biyu da yara hudu, tare da daukar alkawarin samar musu da aikin yi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ibadan, Oyo - Wata tankar mai ta kutsa ayarin motar Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Godswill Akpabio a jihar Oyo.

An tabbatar da cewa lamarin ya yi sanadin mutuwar wani jami’i da ke tare da tawagar da ake kiransu ‘Dispatch riders’ mai suna Ibrahim Hussaini.

Wani jami'i a ayarin motocin Akpabio ya rasa ransa
Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio. Hoto: The Nigerian Senate.
Source: Twitter

Godswill Akpabio ya fadi rashin da ya yi

Akpabio ya bayyana faruwar lamarin ne a zaman Majalisar Dattawa na ranar Talata 23 ga watan Disambar 2025, cewar Premium Times.

Kara karanta wannan

Tinubu ya sa lokacin da sababbin jakadu za su fara aiki bayan amincewar majalisa

Yayin zaman majalisar, Akpabio ya jajanta wa iyalan marigayin bisa wannan babban rashi da suka yi.

‘Dispatch riders’ su ne jami’an ‘yan sanda ne da ke hawa babura a matsayin wani bangare na tsaron manyan jami’an gwamnati.

Shugaban Majalisar Dattawa yana da akalla irin wadannan jami’an guda hudu a ayarinsa.

Ko da yake Akpabio bai bayyana takamaiman inda lamarin ya faru ba, ya ce abin ya faru ne a Ibadan, babban birnin jihar Oyo, bayan ayarinsa sun dauko shi daga filin jirgin saman Ibadan.

Akpabio ya ce:

“Mun je jihar Oyo ne domin halartar bikin nadin wani abokin aikinmu, amma motocin da suka zo daukana daga filin jirgin saman Ibadan… abin takaici, direban tankar mai ya murkushe jami’ina, har kansa ya fashe. Mun riga mun birne shi mintuna 15 da suka wuce a jihar Kogi. Ya bar mata biyu da yara hudu.”
Akpabio ya yi jimamin mutuwar daya daga cikin jami'ai a ayarin motocinsa
Shugaban majalisar dattawa yayin zamansu, Godswill Akpabio. Hoto: Godswill Obot Akpabio.
Source: Facebook

Akpabio ya roki a ba marayu aikin gwamnati

Shugaban Majalisar Dattawan ya roki shugabannin ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati da su bai wa ‘ya’yan marigayin aikin yi kai tsaye.

Kara karanta wannan

Tinubu ta nuna alhini bayan mutuwar tsohon mataimakin shugaban kasa

Ya kara da cewa idan babu guraben aiki a halin yanzu, shi da kansa zai tabbatar da daukar ‘ya’yan aikin yi, cewar TheCable.

“Da yardar Allah, ina ba da shawarar a dauki manyan ‘ya’yansa guda biyu aiki nan take a kowace hukuma da za ta iya. Idan kuma hakan bai yiwu ba, zan dauke su aiki da kaina a cikin harkokina na kashin kai.”

- In ji Akpabio.

Bayan wannan bayani, Sanatan Kogi ta Yamma, Sunday Karimi, ya mike da batun bayanin kai tsaye domin gabatar da lamarin a hukumance a gaban Majalisar Dattawa.

Yayin da yake jajanta wa Akpabio, Karimi ya ce marigayin jami’in tsaron, wanda ke da mukamin DSP, ya kusa yin ritaya a shekara mai zuwa.

Ya bayyana cewa Hussaini, dan asalin jihar Kogi, ya fara aiki a cikin ayarin Akpabio tun daga shekarar 2023, lokacin da ya zama Shugaban Majalisar Dattawa.

Tsohon dan majalisar tarayya ya yi hatsari

Kun ji cewa tsohon dan majalisar tarayya, Hon. Ogbonna Nwuke, ya tsallake rijiya da baya a wani mummunan hatsarin mota.

Kara karanta wannan

'Shirya komai aka yi': An 'gano' yadda rashin tsaro ya fara a Najeriya

Hon. Nwuke ya yi godiya ga Allah bisa yadda ya cece alshi daga hatsarin, wanda ya auku ranar Litinin, 22 ga watan Disamba, 2025.

Rahoto ya nuna cewa motar ta kama da wuta, amma Allah ya cece shi ta hannun wasu mutane da suka kawo dauki.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.