Kano na cikin Alheri, Gwamna Abba Ya Sanya Hannu kan Dokar Kafa Sabuwar Kwaleji

Kano na cikin Alheri, Gwamna Abba Ya Sanya Hannu kan Dokar Kafa Sabuwar Kwaleji

  • Gwamna Abba Kabir Yusuf ya rattaba hannu kan dokar kafa kwalejin Gaya domin fadada ilimi da bunkasa fasaha a Kano
  • Majalisar Kano ta fara amincewa da kudirin bayan rahoton kwamitin mutum 14 da aka nada domin tabbatar da kafa kwalejin
  • Sabuwar makarantar za ta samar da ayyukan yi, karuwar fasaha da ci gaban tattalin arziki ga Gaya da yankunan makwabta

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano - Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a kan dokar kafa kwalejin fasaha ta Gaya, wacce za a yi a karamar hukumar Gaya.

Rahoto ya nuna cewa sanya hannu kan dokar wani muhimmin mataki ne da zai fadada damar karatun gaba da sakandare da kuma bunkasa fasaha a Kano.

Gwamna Abba Yusuf na Kano ya rattaba hannu kan dokar kafa kwalejin Gaya.
Hoton Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya na rattaba hannu kan wasu takardu. Hoto: @Kyusufabba
Source: Twitter

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Juma’a.

Kara karanta wannan

Abba Kabir ya tura 'yan Kano 350 karatu India, ya musu wasiyya mai ratsa zuciya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yunkurin karfafa ilimi da fasaha a Kano

Sanusi Dawakin Tofa ya sanar da cewa an gudanar da bikin rattaba hannun a fadar gwamnati tare da shugabannin majalisar dokoki ta jihar.

Gwamna Abba ya ce kafa kwalejin Gaya wani muhimmin ginshiki ne a burin gwamnatin sa na farfado da ilimi a matakai daban-daban da kuma samar da gajeru da dogayen kwasa-kwasan fasaha ga matasa.

Sanarwar ta rahoto Gwamna Abba Yusuf yana cewa:

“Wannan matakin babbar nasara ce ga yunƙurin mu na inganta ilimi. Kwalejin Gaya za ta bai wa matasanmu damar koyon fasahohi da za su inganta tattalin arziki.”

Gwamnan ya yaba wa majalisar dokoki bisa saurin tabbatar da kudirin, yana mai cewa hakan ya nuna jajircewar su wajen kara inganta ilimi a Kano.

Gudunmawar kwamitin kafa kwalejin Gaya

Kudirin kafa sabuwar makarantar ya fito ne bayan rahoton kwamitin mutum 14 da gwamnatin Kano ta kafa a Agusta 2025 domin tsara dukkanin matakan bude kwalejin.

Kara karanta wannan

Kano: Bayan shekaru 9, kotu ta yanke wa mutum 4 hukuncin kisan ta hanyar rataya

Kwamitin, wanda mataimakin gwamna, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ya kaddamar, ya yi aiki karkashin jagorancin Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa, shugaban jami’ar Northwest.

Mun ruwaito cewa, ayyukan da kwamitin ya gudanar sun hada da:

  • Shirya wa da tura kudirin kafa kwalejin ga majalisa, da tabbatar da amincewa da shi.
  • Neman amincewar hukumar kula da ilimin fasahohi ta NBTE.
  • Kula da fara gina makarantar.
  • Daukar ma’aikata da fara jarabawar shigar karatu ga dalibai.
  • Tattaunawa da masu ruwa da tsaki don ganin kwalejin ta fara aiki.

Tun a lokacin, gwamnatin Abba ta umurci kwamitin da ya tabbatar da kwalejin ta fara karatu kafin zuwan sabuwar shekarar karatu.

Gwamnatin Abba Yusuf ta ce samar da kwalejin Gaya za ta bunkasa ilimin Kano da tattalin arziki.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf. Hoto: @Kyusufabba
Source: Facebook

Amfanin kwalejin Gaya jihar Kano

Dawakin Tofa ya bayyana cewa kafa sabuwar kwalejin fasahar na da nasaba da manufofin gwamnatin Kano na saukaka samun ilimi da kuma bunkasa tattalin arziki a jihar.

A cewarsa, kwalejin za ta samar da dimbin ayyukan yi, habaka fasaha, kirkire-kirkire da kuma inganta tattalin arziki a Gaya da yankunan da ke makwabtaka.

Gwamnatin Kano ta ce wannan mataki wani bangare ne na sabuwar dabarar ilimi da nufin canza fasalin karatun fasaha da kimiyya domin mikawa matasa damar gina rayuwarsu cikin alfahari.

Kara karanta wannan

Bayan rikicin manoma da makiyaya, gwamnati ta dakatar da sarakuna 2 a Gombe

Za a tilasta koyarwa da harshen Hausa

A wani labarin, mun ruwaito cewa, majalisar Kano ta fara duba kudurin doka da zai wajabta koyarwa da harshen Hausa a makarantun jihar.

Hon. Musa Ali Kachako ne ya dauki nauyin kudurin wanda ya ce zai taimaka wajen inganta fahimtar dalibai da rage faduwa a jarrabawa.

Kudurin ya shiga hannun Kwamitin Ilimi na majalisar dokokin domin karin nazari da bayar da shawarwari kafin karatun sa na gaba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com