Kano: Ana Tuhumar Matashi da Hallaka Mahaifinsa kan Hana Shi Kara Mata

Kano: Ana Tuhumar Matashi da Hallaka Mahaifinsa kan Hana Shi Kara Mata

  • Wata babbar kotu a Kano ta umarci a tsare wani matashi a jihar bayan ya hallaka mahaifinsa wanda ya daga hankulan mutane
  • Ana zargin matashin mai suna Aminu Ismail daga Ajingi ya kashe mahaifinsa bayan takaddama kan niyyarsa ta ƙara matar aure
  • An gurfanar da Aminu ƙarƙashin Sashe na 221 bisa doka, kuma kotu ta umarci a ci gaba da tsare shi yayin da shari’a ke gudana

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Wani lamari mai ban mamaki ya faru a jihar Kano bayan zargin wani matashi da kisan mahaifinsa kan wani sabani a tsakaninsu.

Lamarin ya hargitsa makwabtansu duba da darajar da mahaifi ke da shi amma 'dan ya yanke shawarar hallaka shi.

Kotu ta tsare matashi kan zargin kashe mahaifinsa
Kakakin rundunar yan sandan jihar Kano. Hoto: Abdullahi Haruna Kiyawa.
Source: Facebook

Rahoton Aminiya ya tabbatar da faruwar haka da safiyar yau Juma'a 31 ga watan Oktobar 2025 da cewa kotu ta tsare shi.

Kara karanta wannan

Kwamandojin 'yan bindiga sun kaure da fada, shedanin dan ta'adda ya sheka barzahu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda iyaye ke rasa ransu a hannun 'ya'yansu

Ana Najeriya ana yawan yawan samun sabani tsakanin 'ya'ya da iyayensu wanda a karshe ake kai wa ga rasa rai.

A kwanakin baya, wani matashi ya sassara wuyan mahaifinsa a jihar Jigawa lamarin da ya jefa jama'a cikin tashin hankali.

Rundunar 'yan sanda ta Jihar ta tabbatar da cafke matashin da ake zargi da daba wa mahaifinsa adda har ya mutu a ƙaramar hukumar Gwaram.

Lamarin ya faru ne a unguwar Bakin Kasuwa da ke yankin Sara, inda ake zargin matashin mai shekaru 20 ya kai wa mahaifinsa harin da ya jawo rasuwarsa.

An tsare matashi a Kano kan zargin kisan mahaifinsa
Gwamna Abba Kabir na jihar Kano. Hoto: Abba Kabir Yusuf.
Source: Facebook

Kotu ta tsare matashi kan 'kisan' mahaifinsa

Wata babbar kotu a Kano ta ba da umarnin tsare Aminu Ismail, wanda ake zargin ya kashe mahaifinsa sakamakon saɓani kan burinsa na kara aure na biyu.

Matashin da ake zargin ya kashe mahaifin nasa mai suna Malam Dahiru Ahmed ya fito ne daga Unguwar Bai da ke karamar hukumar Ajingi a jihar ta Kano, cewar Daily Post.

Kara karanta wannan

Ajali ya gitta: Saurayi ya mutu daga zuwa zance wurin budurwa a jihar Yobe

Lauya mai gabatar da kara, Barista Abba Lamido Sorondinki ya ce mahaifin ya gargade shi ka da ya ƙara aure saboda halin tattalin arzikin ƙasa, amma lamarin ya rikide zuwa rikici mai zafi.

Zargin da ake yi wa matashin a Kano

Ana zargin Aminu ya caka wa mahaifinsa wuƙa har ya mutu, kuma yanzu yana fuskantar shari’ar kisa a ƙarƙashin Sashe na 221 tare da tsarewa.

A halin yanzu shari'ar na ci gaba da gudana yayin da kotun ta ba da umarnin tsare matashi har zuwa lokacin kammala zaman kotu.

Sai dai har zuwa wannan lokaci rundunar yan sanda ba ta fitar da sanarwa a hukumance kan lamarin da ya afku ba a jihar.

Matashi ya kashe mahaifinsa a Bauchi

A wani labarin, an ji wani matashi mai suna Liman Muhammad Baba ya kashe mahaifinsa Malam Baba Siti a kauyen Uzum da ke jihar Bauchi.

Rahotanni sun bayyana cewa wannan yaro ya doke mahaifinsa da sanda a kai bayan wata gardama da suka yi.

Rundunar ’yan sandan jihar ta tabbatar da kama wanda ake zargin, kuma an gurfanar da shi a gaban kotu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.