Sheikh Kabiru Gombe Ya Samu Sarauta, An Ga Manyan Malamai na Taya Shi Murna a Hotuna

Sheikh Kabiru Gombe Ya Samu Sarauta, An Ga Manyan Malamai na Taya Shi Murna a Hotuna

  • An nada sakataren kungiyar Izala na Najeriya, Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe a sarautar Modibbon Lau a jihar Taraba
  • Fitaccen malamin addinin musuluncin ya karbi takardar wannan nadin sarauta daga hakimin Lau, Alhaji Abdullahi Ibrahim na Chindo
  • Malam Kabir Gombe na daya daga cikin malaman sunnah da suka yi fice wajen karantarwa musamman a mimbarin kungiyar Izala

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Taraba - Fitaccen malamin addinin musuluncin nan, Sheikh Muhammadu Kabiru Haruna Gombe ya samu sarauta a jihar Taraba da ke Arewa maso Gabashin Najeriya.

An nada Sheikh Kabiru Gombe, sakataren kungiyar Jama'atu' Izalatil Bidi'a Wa Iqamatus-Sunnah (JIBWIS) a sarautar Modibbon Lau.

Sheikh Muhammadu Kabiru Haruna Gombe.
An ba Kabir Gombe sarautar Modibbon Lau a jihar Taraba Hoto: Jibwis Nigeria
Source: Facebook

Kungiyar JIBWIS ta Najeriya wacce aka fi sani da Izala ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta wallafa tare da hotuna a shafin Facebook.

Kara karanta wannan

Sanata Barau ya tabo kujerar Gwamnan Abba a gangamin zaben cike gurbin Kano

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An nada Sheikh Kabiru Gombe a sarauta

Sanarwar ta ce hakimin Lau da ke karamar hukumar Lau a jihar Taraba, Alhaji Abdullahi Ibrahim na Chindo ya amince da nadin Malam Kabiru a matsayin Modibbon Lau.

A hotunan da kungiyar Izala ta wallafa, an ga Sheikh Kabir Gombe dauke da takardar nadin sarautar da aka masa a hukumance.

Hotunan sun kuma nuna yadda manyan malaman kungiyar Izala suka taya Kabiru Gombe murnar samun wannan sarauta.

Malaman Izala sun taya Kabiru Gombe murna

Daga cikin wadanda aka gani suna taya malamin murna akwai shugaban kungiyar Izala na Najeriya, Sheikh Abdullahi Bala Lau.

Sauran sun hada da shugaban Izala na jihar Kano kuma shugaban hukumar alhazai ta kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan da wasu malamai da alarammomi.

Kungiyar Izala ta fitar da sanarwa

Sanarwar ta ce:

"Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe ya zama sabon Modibbon Lau.

Kara karanta wannan

Tinubu ya sakawa kanwar Abdussamad BUA, ya ba ta mukami a gwamnatinsa

"Mai girma hakimin Lau, Alh Abdullahi Ibrahim na chindo, ya naɗa babban sakataren kungiyar JIBWIS, Sheikh Dr. Muhammad Kabir Haruna Gombe, a matsayin ‘Modibbon Lau’.
"A madadin ƙungiyar Izala, muna taya shi murna tare da addu’an Allah ba shi ikon sauke nauyin da aka ɗora masa. Amin."
Sheikh Kabiru Gombe tare da malaman Izala.
Yadda manyan malamai suka taya Sheikh Kabiru Gombe murna Hoto: Jibwis Nigeria
Source: Facebook

Takaitaccen bayani kan Sheikh Kabiru Gombe

Sheikh Kabiru Gombe dai yana daya daga cikin malaman Izala da suka shahara a Najeriya, nahiyar Afirka da ma duniya baki daya.

Malamin ya fito daga jihar Gombe da ke Arewa maso Gabashin Najeriya kuma ya zama sakataren Izala na kasa tun daga watan Disamba, 2011 zuwa yau.

Mutane da dama sun taya Sheikh Kabiru Gombe murnar wannan nadi tare fatan Allah Ya sa hakan ya kara masa kwarin gwiwar ci gaba da karantarwa.

Sheikh Bashir Aliyu ya zama shugaban SCSN

A wani labarin, kun ji cewa Majalisar Shari’ar Musulunci ta Najeriya (SCSN) ta sanar da naɗin Sheikh (Dr.) Bashir Aliyu Umar, a matsayin sabon Shugabanta na ƙasa.

Hakan dai na zuwa ne bayan rasuwar tsohon shugaban majalisar, Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah, wanda aka bayyana a matsayin rashi ga al’ummar Musulmi a Najeriya da ma duniya baki ɗaya.

Fitaccen malamin musulunci daga Kano, Dr. Bashir sananne ne a fagen ilimin addinin islama da kuma tsarin harkokin kuɗi a Musulunci a Najeriya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262