‘Ku Ƙaura’: Ambaliya Za Ta Yi Ɓarna a Sokoto, Yobe, Neja da Jihohi 17 a Watan Yuli

‘Ku Ƙaura’: Ambaliya Za Ta Yi Ɓarna a Sokoto, Yobe, Neja da Jihohi 17 a Watan Yuli

  • Hukumar NiMet ta gargadi jihohi 20 game da yiwuwar ambaliyar ruwa a watan Yuli 2025, inda Sokoto ke cikin matsanancin haɗarin ambaliyar
  • Hukumar ta lissafa Kaduna, Zamfara, Yobe, da sauran jihohi 16 a matsayin jihohin da za su iya fuskantar ambaliyar ruwa a cikin wannan wata
  • NiMet ta ba da shawarwari kan tsaftace magudanan ruwa, guje wa tuki yayin da ake ruwa, da yin kaura daga wuraren da ambaliya za ta shafa

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja – Hukumar kula da hasashen yanayi ta Najeriya (NiMet) ta fitar da gargadi ga al'ummar ƙasar game da yiwuwar ambaliyar ruwa a watan Yuli na shekarar 2025.

Hukumar ta bayyana cewa, bisa ga hasashen yanayi na kakar ruwa (SCP), akwai manyan yankuna da ke fuskantar barazanar ambaliya.

Kara karanta wannan

Rikici ya ɓarke da Aminu Ado Bayero ya zo wucewa ta Fadar Sarki Sanusi II a Kano

NiMet ta ce akwai yiwuwar ambaliya ta afku a Sokoto, Kaduna da wasu jihohi 18
Wani gari a cikin garuruwan Najeriya da ambaliyar ruwa ta mamaye. Hoto: Audu Marte
Source: Facebook

Jihohohi 20 na cikin haɗarin ambaliyar ruwa

NiMet ta lissafa jihohin Najeriya 20 da za su iya fuskantar ambaliya a sanarwar hasashen da ta fitar a shafinta na X a ranar Litinin, 7 ga Yuli.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar sanarwar da NiMet ta fitar, jihar Sokoto ce ke kan gaba a jerin jihohin da ke cikin haɗarin gaske na fuskantar ambaliyar ruwa.

Wannan yana nuna bukatar gaggawa ga mazauna jihar da hukumomin yankin da su ɗauki matakan kariya daga afkuwar mummunar ambaliya.

Bayan jihar Sokoto, akwai wasu jihohi 19 da NiMet ta lissafa a matsayin wadanda za su iya gamuwa da ambaliyar

Jihohin da ke fuskantar matsakaicin haɗarin ambaliya

  1. Kaduna
  2. Zamfara
  3. Yobe
  4. Bauchi
  5. Bayelsa
  6. Jigawa
  7. Adamawa
  8. Taraba
  9. Niger
  10. Nasarawa
  11. Benue
  12. Ogun
  13. Ondo
  14. Lagos
  15. Delta
  16. Edo
  17. Cross River
  18. Rivers
  19. Akwa Ibom

Wannan jerin ya shafi jihohi da dama a sassan ƙasar, wanda ke nuna cewa ambaliyar ruwa na iya zama babbar barazana ga yankuna daban-daban a cikin watan Yuli.

Kara karanta wannan

An shiga firgici a Gombe: Mutane 4 sun mutu, gidaje 171 sun rushe sakamakon ambaliya

Shawarwari daga NiMet don kare kai

Domin rage illolin ambaliyar ruwa, NiMet ta ba da shawarwari masu muhimmanci ga jama'a:

1. Tsaftace magudanan ruwa: A tabbatar da cewa an kwashe magudanan ruwa a yankunan gidaje da muhallai don hana taruwar ruwa.

2. A guji tuƙi ko zirga-zriga idan ana ruwa: Kada a yi tuƙi ko tafiya a cikin ruwan da ake sa ran zai haifar da ambaliya, a cewar NiMet zai iya zama mai haɗari.

Hukumar NiMet ta ba da shawarwari yayin da aka hango jihohi 20 da ambaliya za ta shafa
Wani sashe na jihar Borno da ya nutse a cikin yayin ambaliyar madatsar Alau a 2024. Hoto: Audu Marte
Source: Getty Images

3. A kaura idan babu mafita: Idan aka ga alamar haɗarin ambaliya a waje, to a gaggauta yin ƙaura zuwa wuri mafi aminci.

4. A tanadi kayayyakin bukatu: NiMet ta bukaci jama'a su tanadi kayan bukatu na gaggawa kamar su abinci, ruwa, kayan agajin lafiya, da takardu masu muhimmanci.

5. Kashe lantarki da gas: A kashe wutar lantarki da gas din girki nan take idan aka ga alamun ambaliyar ruwa.

6. Ƙarfafa rigakafin zaizaya: A ɗauki matakai don hana zaizayar ƙasa, musamman a yankunan da ke da tudu.

Kara karanta wannan

Kaduna: SDP ta yi babban rashi, jagoranta ya rasu a mummunan hadarin mota

7. Wayar da kan al'umma: A haɓaka wayar da kan jama'a game da haɗarin ambaliyar ruwa da matakan kariya.

8. Ɗaukar mataki da wuri: Kada a jira har lamarin ya yi muni kafin a ɗauki mataki.

Don samun ƙarin bayani, jama'a za su iya ziyartar shafin NiMet a www.nimet.gov.ng ko kuma su bi shafukan su na sada zumunta.

Manyan Arewa sun ba da mafita kan ambaliya

A wani labarin, mun ruwaito cewa, kungiyar ACF ta ja hankalin gwamnati kan buƙatar ɗaukar matakan kariya tun kafin ambaliyar da ake hasashen zata faru a daminar bana.

Shugabannin Arewa sun bukaci gwamnati a matakin tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi da su shirya tsaf don rage illar ambaliya.

ACF ta kuma shawarci mazauna yankunan da ke cikin haɗarin ambaliya da su kiyaye muhalli, su guji toshe hanyoyin ruwa da kuma gyara gidajensu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com