Katsina: Biki Ya Koma Makoki bayan Bindige Ɗan Shekara 10, an Harbi Budurwa a Kwankwaso

Katsina: Biki Ya Koma Makoki bayan Bindige Ɗan Shekara 10, an Harbi Budurwa a Kwankwaso

  • Harbin bindiga ya auku a wajen bikin aure a Unguwar Liman, Magama Jibia, Katsina, inda yaro dan shekara 10 ya rasa ransa
  • Wani mamba na kungiyar masu farauta ya harba bindiga wanda ya hallaka yaron Malam Yusuf, ya jikkata Shamsiyya Salisu mai shekara 25
  • Rundunar ‘yan sanda ta cafke Adamu Idris da ake zargin ya yi harbin da bindigar toka, an kwato harsashi daya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Katsina - Wani bikin daurin aure ya koma jimami a jihar Katsina da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa wani yaro mai shekaru 10 ya mutu sanadin harbin bindiga ana tsaka da bikin.

Harbin bindiga ya kashe dan shekara 10 a Katsina
Dan banga ya harbi dan shekara 10 a Katsina a bikin aure. Hoto: Nigeria Police Force.
Source: Facebook

Rahoton Zagazola Makama ya tabbatar da cewa lamarin ya auku yayin bikin aure a Unguwar Liman, Magama Jibia da ke jihar Katsina.

Kara karanta wannan

Allah sarki: Yan bindiga sun kai hari, sun hallaka basarake da wasu mutum 2

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kura- kurai da ake samu na harba bindiga

Wannan ba shi ne karon farko ba da ake samun kuskure daga wasu yan banga da ke hallaka mutane duk da ana kyautata zaton ba da gangan ba ne.

Ba yan banga kadai ba har jami'an tsaro a Najeriya na samun irin wannan kuskure wanda ke jawo rashin hankali a tsakanin mutane.

Hakan ke sa ake daukar mummunan mataki idan hakan ta faru domin tabbatar da kare afkuwar matsalar a gaba.

An hallaka yaro yayin biki a Katsina

Majiyar da muka samu ta ce harbin bindigar ya hallaka yaron dan shekara 10 inda wata yarinya ta samu rauni.

Lamarin ya faru a ranar 7 ga Yuli da misalin karfe 2:50 na rana a bikin aure na daya daga cikin mambobin kungiyar mafarauta.

An ce wani mutum mai shekara 45 mai suna Adamu Idris ya harba bindigar toka yayin shagalin, harsashin ya samu Yusuf a ciki.

Kara karanta wannan

Katsina: Ƴan bindiga sun yi shigar dare, sun sace Sarki yayin wani farmaki

Harsashin ya kuma jikkata wata yarinya mai suna Shamsiyya Salisu ‘yar shekara 25 a kunkuminta, lamarin da ya girgiza mahalarta bikin.

Yan sanda sun cafke dan banda bayan kashe yaro
Dan banga ya harbe yaro har lahira a Katsina. Hoto: Legit.
Source: Original

Matakin da yan sanda suka dauka da gaggawa

‘Yan sanda daga ofishin Jibia sun isa wurin cikin gaggawa, aka garzaya da wadanda lamarin ya rutsa da su zuwa Asibitin Gwamnati na Jibia.

A can ne likita ya tabbatar da mutuwar Malam Yusuf, yayin da aka fara ba Shamsiyya kulawa a halin yanzu a asibitin.

An cafke wanda ake zargi, Adamu Idris, nan take, kuma an kwato bindigar da harsashi daya.

Rundunar ‘yan sanda ta bayyana cewa bincike ya fara, kuma za a gurfanar da wanda ake zargin da zarar an kammala binciken.

Dan banga ya harbi matashi a Borno

Mun ba ku labarin cewa an harbe wani matashi da bindiga a lokacin bikin naɗin sarauta a Gwoza, jihar Borno da ke Arewa maso Gabashin Najeriya.

Lamarin ya faru ne ana bikin nadin sarauta inda Yusuf Ahmadu ya harbe Isa Ali da gangan lokacin da ya karɓi bindiga daga wani jami'in sa-kai, Buba Hamman a wurin bikin.

An kai wanda aka harba asibitin Gwoza, likitoci suka tabbatar da mutuwarsa inda yan sanda sun kama Ahmadu da Hamman don bincike.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.