"Ba Ruwan Ƴan Bindiga," Gwamna Ya Kawo Karshen Jita Jita, Ya faɗi Wanda Ya Kashe Ƴar Uwarsa

"Ba Ruwan Ƴan Bindiga," Gwamna Ya Kawo Karshen Jita Jita, Ya faɗi Wanda Ya Kashe Ƴar Uwarsa

  • Gwamna Agbu Kefas na jihar Taraba ya bayyana gaskiya kan yadda aka kashe ƴar uwarsa, Atsi Kefas a hanyar zuwa Abuja a 2024
  • Kefas ya ce wani ɗan sanda da ke gadin ayarin mahaifiyarsa ne ya ɗana bindiga, ya harbi ƴar uwarsa daga kusa-kusa, amma ba ƴan bindiga ba ne
  • Galibin mazauna jihar Taraba sun ɗauka ƴan bindiga ne suka faramaki mahaifiyar gwamnan da yar uwarsa da nufin yin garkuwa da su

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Taraba - Gwamnan jihar Taraba, Dr. Kefas Agbu, ya bayyana yadda 'yar uwarsa, Atsi Kefas, ta rasu, wanda ake zargin ƴan bindiga ne suka harbe ta a titin Wukari-Chinkai.

Gwamna Kefas ya bayyana cewa wani ɗan sanda da ke gadin mahaifiyarsa ne ya kashe ƴar uwarsa a hanyarsu ta zuwa Abuja daga Jalingo a shekarar da ta gabata, 2024.

Kara karanta wannan

Abin ba daɗi: Ministan Tinubu ya bayyana yadda aka kashe mahaifinsa a jihar Kaduna

Gwamna Agbu Kefas.
Gwamnan Taraba ya ce ba ƴan bindiga ba ne suka kashe ƴar uwarsa Hoto: Agbu Kefas
Source: Twitter

Mai girma gwamnan ya faɗi haka ne yayin da yake zantawa da manema labarai a Jalingo, babbar birnin jihar Taraba, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Yadda aka yi ajalin ƴar uwar Gwamna Kefas

Kefas ya ce lamarin ya faru ne a shekarar 2024 a kan titin Wukari-Chinkai, lokacin da Atsi ke hanyar zuwa Abuja daga Jalingo tare da mahaifiyarsu.

“A bara, ‘yar uwata Atsi tana cikin mota tare da mahaifiyata, ana zaton cewa 'yan bindiga ne suka kai musu hari, amma bincike ya nuna ɗan sanda da ke tare da su ne ya harbe ta,” in ji Gwamna Kefas.

Ya ƙara da cewa an gano guntun kwankon harsashi a jikin Atsi lokacin da likitoci ke kokarin ceton rayuwarta kafin daga bisani ta rasu.

Mutane da dama a jihar Taraba sun yi imanin cewa ‘yan bindiga ne suka kai hari kan motar da ke ɗauke da Atsi da mahaifiyar gwamna, suna kokarin yin garkuwa da su.

Kara karanta wannan

Nahiyar Afirka ta yi babban rashi, fitaccen marubuci ya riga mu gidan gaskiya

Wane mataki aka ɗauka kan ɗan sandan?

“Rayuwa tana da muhimmanci ƙwarai a wurina. Ba zai yiwu ka kashe rai kai tsaye ba, kuma ka sa ran Allah zai yarda da kai.
"‘Yar uwata karama ta mutu ne sakamakon harbin ɗan sanda, kuma suna cikin mota daya,” in ji shi.

Gwamna Kefas ya kuma bayyana cewa jami’in dan sandan da ake zargi na nan ana ci gaba da gudanar da bincike a kansa domin a tabbatar da adalci, in ji Leadership.

Gwamna Kefas.
Gwamna Kefas ya nuna ɓacin ɗansa bisa abin da ya faru a Karim-Lamido Hoto: Agbu Kefas
Source: Twitter

Kefas ya nuna damuwa da rikicin Karim-Lamiɗo

A cikin taron, gwamnan ya yi shirun minti daya domin girmama Atsi da kuma fiye da mutane 50 da aka kashe kwanan nan a karamar hukumar Karim-Lamido.

“Muna bukatar zaman lafiya da soyayya a tsakaninmu. Ya kamata mutane su zauna lafiya, su zauna da juna cikin aminci domin ci gaban yankinsu.
"Amma abin takaici wasu sun rungumi rikici wanda ba abin da yake haifarwa sai asarar rayuka," In ji Kefas.

Kara karanta wannan

"Ya gaza": Tsohon gwamna ya caccaki Tinubu kan kuntatawa 'yan Najeriya

Gwamnan ya kuma bayyana cewa zai kafa kwamitin bincike domin gano musabbabin rikicin da ya auku a Karim-Lamido da kuma samar da zaman lafiya mai ɗorewa a yankin.

Mataimakin gwamnan Taraba ya koma gida

A wani labarin, kun ji cewa Mataimakin gwamnan Taraba, Alhaji Aminu Alkali, ya dawo Jalingo bayan kusan wata hudu yana jinya a Abuja da kasar Masar.

Dawowar mataimakin gwamnan ta kawo ƙarshen tsawon lokacin da aka yi ba tare da an ji ɗuriyarsa ba, lamarin da ya haddasa kace-nace tsakanin al'umma.

Rahotanni sun nuna cewa Aminu Alkali ya sauka a Filin Jirgin Sama na Danbaba Suntai a Jalingo, a jirgin haya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262