'Akwai Alheri': Gwamna Ya Fadi Albarkar da Ke cikin Cire Tallafin Mai, Ya Shawarci Gwamnoni

'Akwai Alheri': Gwamna Ya Fadi Albarkar da Ke cikin Cire Tallafin Mai, Ya Shawarci Gwamnoni

  • Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, ya yi magana kan alherin da gwamnoni suke samu bayan cire tallafin man fetur a watan Mayun 2023
  • Uzodinma ya ce cire tallafin man fetur rahama ne ga gwamnatocin jihohi don samun karin kudi saboda gudanar ayyukan ci gaba a jihohinsu
  • Gwamnan ya bayyana cewa cire tallafin ya kawo karin kudi ga jihohi, wanda zai taimaka wajen bunkasa ababen more rayuwa da jin dadi
  • Ya bukaci jihohi su yi amfani da karin kudaden don tabbatar da cigaban jama’a, musamman bayan cire tallafin da Gwamnatin Tarayya ta yi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Owerri, Imo - Duk da korafe-korafe daga al'ummar Najeriya, Gwamna Jihar Imo, Hope Uzodimma, ya fadi alherin da cire tallafin man fetur ya jawo musu.

Gwamna Uzodinma ya bayyana cewa cire tallafin man fetur wata babbar rahama ce ga gwamnatocin jihohin Najeriya saboda alherin da suke samu.

Kara karanta wannan

'Ku bar wadaƙa da dukiyar al'umma': Sanatan APC ga gwamnonin Arewa kan haraji

Gwamnan APC ya fadi alherin da ke cikin cire tallafin mai
Gwamna Hope Uzodinma ya shawarci gwamnoni kan amfani da kudin cire tallafin mai. Hoto: Hope Uzodinma.
Asali: Twitter

Channels TV ta ce Gwamnan ya yi wannan bayani ne a jiya Litinin 13 ga watan Janairun 2024 a Imo yayin duba wasu ayyuka domin bikin cika shekara guda a wa’adin sa na biyu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya magantu bayan cire tallafin mai

Hakan ya biyo bayan maganar da shugaban kasa, Bola Tinubu ya sake yi game da cire tallafin mai a yayin jawabinsa ga yan kasa.

A yayin jawabin, Tinubu ya ce babu nadama kan cire tallafin man fetur a watan Mayu 2023 da ya yi a Najeriya.

Tinubu ya bayyana cewa cire tallafin ya kawo gasa a bangaren man fetur, inda farashin ya fara raguwa a wurare daban-daban.

Ya jaddada cewa bai aminta da kayyade farashi ba, yana mai cewa za a ci gaba da kokarin samar da isasshen fetur.

Gwamna ya fadi alherin cire tallafin mai

A cewarsa, wannan matakin ya ba da damar samun karin kudi ga jihohi don yin aiki mai ma’ana wajen cigaban al’umma da jihohinsu.

Kara karanta wannan

Bankin duniya ya fitar da sabon hasashe a kan tattalin arzikin Najeriya

Uzodinma ya bayyana cewa karin kudaden da ake samu yanzu zai taimaka wajen samar da kayayyakin more rayuwa, habaka kasuwanci, da jin dadin jama’a.

Gwamnan na APC ya kara da cewa jihohi yanzu suna da damar yin aiki da karin kudin da suka samu daga cire tallafin man fetur, cewar Daily Post.

Ya yi kira ga gwamnatocin jihohi su tabbatar sun yi ayyukan da za su amfani al’umma, duba da karin kudaden da suke samu daga gwamnati.

Legit Hausa ta tattauna da mai fashin baki

Kwamred Isma'il Abubakar ya koka kan kalaman Gwamna Hope Uzodinma inda ya ce ya san za a rina.

Kwamred Abubakar ya yi mamaki yadda gwamnoni suka yi shiru lokacin da za a cire tallafin man fetur.

"A yanzu suna ta korafi kan kudirin haraji saboda zai illata su amma lokacin cire tallafi har goyon baya suke yi saboda aljihunsu."

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta fadi dalilin da zai sa a sauke farashin fetur

- Kwamred Isma'il

Mai fashin bakin ya ce ashe da walakin goro a miya, suna samun kuɗi shiyasa ba su yi wata gardama kan cire tallafin ba.

Gwamnan ya ba yan kasa shawara kan haraji

A baya, kun ji cewa Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ya yi kira ga ƴan Najeriya su ware lokaci su karanta baki ɗaya abin da ke kunshe a kudirin harajin Bola Tinubu.

Hope Uzodinma ya ce bai dace mutane su tsaya suna sukar kudirin a cikin duhu ba tare da sanin alherin ko akasin haka da ya ƙunsa ba.

Gwamnan ya bayyana cewa a ganinsa kudirin yana da amfani domin wani tsari ne da zai kawo ƙarin kuɗin shiga ga gwamnati.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.