Cin Hancin $500,000: Tsohon Dan Majalisar Kano Ya Shaki Iskar Yanci, Ya bar Gidan Yari

Cin Hancin $500,000: Tsohon Dan Majalisar Kano Ya Shaki Iskar Yanci, Ya bar Gidan Yari

  • Tsohon dan Majalisar Tarayya a jihar Kano, Farouk Lawan ya shaki iskar yanci bayan zargin cin hanci da rashawa
  • An zargin tsohon dan Majalisar da karbar cin hanci na makudan kudi har $3m a hannun dan kasuwa, Femi Otedola
  • Wannan na zuwa ne bayan daure tsohon dan Majalisar har na tsawon shekaru biyar a gidan gyaran hali

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Tsohon dan Majalisar Tarayya daga jihar Kano, Hon. Farouk Lawan ya shaki iskar yanci.

An zargi Hon. Farouk Lawan da nema da kuma karbar cin hanci na makudan kudi har $500,000.

Tsohon dan Majalisar Tarayya a Kano ya samu yanci bayan daurin shekaru 5
Tsohon dan Majalisar Tarayya, Hon. Farouk Lawan ya shaki iskar yanci. Hoto: Farouk Lawan.
Asali: Facebook

Kano: Zargin da ake yi kan Farouk Lawan

Kara karanta wannan

Gyaran tattalin arziki: Manyan nasarori 5 da gwamnatin Tinubu ta samu a 2024

Punch ta ruwaito cewa Kotun Koli ta tabbatar da hukuncin da aka yanke kan zargin Farouk a ranar 26 ga watan Janairun 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An same shi da laifin karbar $3m daga fitaccen dan kasuwa a bangaren man fetur, Femi Otedola.

Lamarin ya faru ne lokacin da Farouk Lawan ke riƙe da shugaban kwamitin binciken badakalar tallafin mai a 2012.

Daily Nigerian ta wallafa wani faifan bidiyon Hon. Farouk Lawan bayan sakinsa a yau Talata 22 ga watan Oktoban 2024 a shafinta na X.

Karanta wasu labarai game da Farouk Lawan

Kara karanta wannan

Bobrisky: Asirin shahararren Ɗan daudu ya tonu yana shirin tserewa a iyakar Najeriya

Kotu ta ragewa Farouk zaman gidan kaso

A baya, kun ji cewa Kotun daukaka kara da ke Abuja ta yanke wa tsohon dan majalisa, Farouk Lawan, hukuncin bayan gamsuwa da cewa ya amshi rashawar $500,000 a 2012.

An yanke wannan hukuncin ne a ranar Alhamis 24 ga watan Fabrairun 2022 bayan kotun ta wanke dan majalisar daga laifuka biyu da aka daure shi akan su.

Dakyar kotun ta amince da wannan hukuncin sannan ta rage masa lokacin da zai yi a gidan gyaran halin, daga shekaru 7 zuwa shekaru 5.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.