Fitattun ‘Yan Siyasar Kudancin Najeriya da Za Su Iya Kalubalantar Tinubu a 2027

Fitattun ‘Yan Siyasar Kudancin Najeriya da Za Su Iya Kalubalantar Tinubu a 2027

  • Manyan 'yan siyasar Najeriya na ci gaba da wasa wukarsu da kuma tamke ɗamari domin tunkarar babban zaben 2027 da ke tafe
  • Akwai 'yan siyasa daga jam'iyyun adawa da ake sa ran za su kalubalanci Shugaba Bola Tinubu a yunkurinsa na neman tazarce
  • Har yanzu dai masana na ganin cewa Shugaba Bola Tinubu, wanda tsohon gwamnan jihar Legas ne shi ne jagaban siyasar Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - 'Yan siyasa a Najeriya sun fara daura damarar tunkarar zaben shugaban kasa na 2027 da ke tafe.

Ana sa ran Bola Tinubu, wanda shi ne shugaban kasar Najeriya a yanzu zai nemi tazarce a 2027. A lokacin zai ki shekaru 75 a duniya.

Kara karanta wannan

Nasarawa: NASIEC ta shirya gudanar da zaben ciyamomi, an fitar da jadawali

Tinubu na iya fuskantar hamayya daga wasu jiga jigan 'yan siyasar Kudu a zaben 2027.
Peter Obi da wasu manyan 'yan siyasar Kudu da za su iya ba Tinubu matsala a 2027. Hoto: @aonanuga1956
Asali: Twitter

A wannan rahoton, Legit.ng ta zayyano bayanan wasu manyan 'yan sandar Kudancin Najeriya da za su iya kararawa da Tinubu a 2027.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Peter Obi

Jagoran jam'iyyar Labour (LP), Peter Obi ya kasance dan takarar shugaban kasa a zaben 2023 da ya gabata.

A shekarar 2019, Peter Obi ya yiwa Atiku Abubakar mataimaki a neman takarar zaben shugaban kasa karkashin jam'iyyar PDP amma suka sha kasa.

Dan shekaru 63, Peter Obi ya yi fice musamman a wajen matasa bayan hada gangamin 'yan Obidient'.

Ana ganin Peter Obi zai iya ba da Bola Tinubu matsala a 2027 saboda Kudu maso Gabas za ta so yin shugaban kasa, kasancewar ba ta yi ba tun daga 1999.

2. Nysom Wike

Nysom Wike wanda shi ne ministan babban birnin tarayya Abuja, cikakken dan jam'iyyar PDP ne.

Kara karanta wannan

Najeriya @64: Muhimman abubuwa 5 da Tinubu zai yi domin ceto kasa a halin kunci

Wike mai shekaru 56 na daya daga cikin manyan 'yan siyasar Kudancin Najeriya.

Duk da cewa ana ganin kamar yana biyayya ga Tinubu a yanzu amma ana hasashen zai iya tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027.

3. Adewole Adebayo

Barista Adebayo ya kasance mai sharhi kan harkokin al'umma wanda kuma ke ba sa shawarwari kan yanayin siyasa da makomar Najeriya.

Adebayo, wanda dan asalin jihar Ondo ne ya nemi takarar shugaban kasa karkashin jam'iyyar SDP a zaben 2023.

Bayan gaza samun nasara a 2023, an ce Adebayo ya shirya tsaf domin tunkarar zaben 2027.

4. Dan Nwanyanwu

Dan Nwanyanwu ya kasance dan asalin Imo ne kuma shi ne shugaban jam'iyyar Zenith Labour (ZLP).

Ya rike shugaban jam'iyyar Labour (LP) daga shekarar 2004 zuwa 2014.

Nwanyanwu shi ne dan takarar shugaban kasa a zaben 2023 karkashin jam'iyyar ZLP amma bai samu kuri'u masu yawa ba.

Kara karanta wannan

Najeriya @64: Ahmadu Bello da wasu mutane 9 da suka yi fafutukar samun ‘yanci

An fara tallar Tinubu gabanin 2027

A wani labarin, mun ruwaito cewa allunan da ke tallata shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu domin zaɓen 2027 sun fara bayyana a babban birnin tarayya Abuja.

Allunan waɗanda ke ɗauke da hoton Tinubu da uwargidan gidansa Remi Tinubu sun nuna aniyar shugaban ƙasan na neman tazarce a zaben 2027 da ke tafe.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.