Ahmad Isa: Mai Gabatar da Shirin Rai Dangin Goro a Gidajen Rediyo Ya Kwanta Dama

Ahmad Isa: Mai Gabatar da Shirin Rai Dangin Goro a Gidajen Rediyo Ya Kwanta Dama

  • Mun samu rahoton cewa Allah ya yiwa fitaccen dan jaridar Najeriya da ke gabatar da shirin Rai Dangin Goro, Ahmad Isa rasuwa
  • Marigayin wanda dan asalin karamar hukumar Koko Basse ne da ke jihar Kebbi ya rasu a birnin Legas bayan doguwar jinya
  • Kafin rasuwarsa, an ce Ahmad Isa Koto ya shahara a wajen karanta littattafan Hausa a gidaje rediyo musamman na jihar Kano

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Legas - Rahotanni sun bayyana cewa Allah ya karbi rayuwar shahararren mai gabatar da shirin 'Rai Dangin Goro,' Ahmad Isa Koto.

Wasu makusantan marigayin sun bayyana cewa fitaccen mai karanta littattafan adabin Hausa a gidajen rediyon ya rasu ne a birnin Legas.

Kara karanta wannan

Rai ɓakon duniya: Hadimin Gwamna Dikko Radda ya kwanta dama a Katsina

Allah ya yiwa Ahmad Isa, mai gabatar da shirin Rai Dangin Goro rasuwa
Mai gabatar da shirin 'Rai Dangin Goro' a Ahmad Isa ya rasu. Hoto: Sunusi A. Ɗantalata
Asali: Facebook

Ahmad Isa Koto ya kwanta dama

Fitaccen dan jaridar da ya kware a nishadantar da masu saurare ta hanyar sarrafa muryarsa wajen karanta litattafai ya rasu bayan doguwar rashin lafiya, inji rahoton BBC Hausa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Marigayi ahmad Isa Koto ya kasance ma'aikaci ne a gidan rediyon muryar Najeriya wanda aka fi sani da VON.

An ruwaito cewa marigayin wanda dan asalin karamar hukumar Koko Besse ne da ke jihar Kebbi, ya rasu yana da shekaru 61.

Tasirin shirin 'Rai Dangin Goro'

Zai yi matukar wahala ka samu wani matashi a Arewacin Najeriya, musamman ma a jihar Kano da zai ce bai san muryar Ahmad ba, muddin yana sauraron rediyo.

Shirinsa na 'Rai Dangin Goro' na daga cikin manyan shirye-shiryen rediyo da suka yi shuhura kuma suka samu miliyoyin masu sauraro musamman ma mata.

Marigayi Ahmad yana amfani da kwarewarsa da kuma fasahar da Allah ya ba shi ta sarrafa harshe wajen gabatar da shirin Rai Dangin Goro, wanda ke jan hankalin miliyoyin mutane.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.