Da duminsa: Marubuciyar litattafan Musulunci, Aisha Lemu ta rasu

Da duminsa: Marubuciyar litattafan Musulunci, Aisha Lemu ta rasu

Allah ya yiwa shahararriyar malama, marubuciyyar littafan addinin musulunci kuma wadda ta kafa kungiyar mata musulmi na tarayya, FOMWAN, Aisha Lemu rasuwa.

Aisha Lemu ta rasu tana da shekaru 79 a duniya.

Daily Nigerian ta ruwaito cewa Lemu ta rasu ne a yau Asabar a garin Minna, babban birnin jihar Neja.

Da duminsa: Marubuciyar litattafan Musulunci, Aisha Lemu ta rasu
Da duminsa: Marubuciyar litattafan Musulunci, Aisha Lemu ta rasu
Asali: Facebook

DUBA WANNAN: 'Yan ta'addan sun kwace iko da kananan hukumomi 8 a jihar Katsina

Direkta Janar na hukumar NITDA, Sheikh Isa Pantami shima ya tabbatar da rasuwarta inda ya yi addua'ar Allah ya gafarta ma ta.

Marigayiyar mata ce ga Sheikh Ahmad Lemu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel