Awanni bayan Harin 'Yan Boko Haram, Sojoji Sun Dura Garin da Aka Kashe Mutane 87

Awanni bayan Harin 'Yan Boko Haram, Sojoji Sun Dura Garin da Aka Kashe Mutane 87

  • Rahotanni sun bayyana cewa sojojin Najeriya sun kwashe gawarwakin mutanen 37 daga cikin 87 da ake zargin mayakan Boko Haram sun kashe
  • Mataimakin gwamnan Yobe, Idi Barde Gubana zai jagoranci jami’an gwamnati domin halartar jana’izar mutanen 37 a fadar Sarkin Babbangida
  • Tun da fari an ruwaito cewa 'yan ta'addan Boko Haram sun kashe gomman mutane a harin da suka kai Mafa da ke yankin Arewa ta gabas

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Yobe - An kwashe gawarwakin mutanen 37 da mayakan Boko Haram suka kashe daga garin Mafa da ke karamar hukumar Tamuwa a jihar Yobe.

Majiyoyi sun bayyana cewa an kai gawarwakin mutanen da aka kashe zuwa babban asibitin Babbangida kafin a yi jana’izarsu da karfe 10 na safe.

Kara karanta wannan

Miyagun ƴan bindiga sun hallaka babban hadimin shugaban majalisa a Najeriya

Sojoji sun kwashe gawarwakin mutanen da aka kashe a jihar Yobe
Yobe: Sojoji sun kwashe gawarwaki 37 da Boko Haram ta kashe a Mafa. Hoto: AUDU MARTE / Contributor
Asali: Getty Images

Majiyoyi daga al’ummar yankin sun shaida wa jaridar Daily Trust cewa 'yan ta'addan Boko Haram sun kashe akalla mutane 87.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sojoji sun kwaso gawarwaki a Yobe

Mataimakin gwamnan Yobe, Idi Barde Gubana zai jagoranci jami’an gwamnati domin halartar jana’izar a fadar Sarkin Babbangida, hedikwatar karamar hukumar Tarmuwa.

Wata majiya ta bayyana cewa:

“Mun samu tabbacin cewa sun kashe akalla mutane 87. Ba za mu iya nuna muku gawarwakin wadanda aka kashe ba saboda wasu sun mutu a daji, har sojoji sun kasa gano su."

Hare-haren mayakan Boko Haram

Majiyar ta ci gaba da cewa:

“Ya zuwa yanzu gawarwaki 37 suna babban asibitin Babbangida bayan da sojoji suka kwashe su daga cikin garin da abin ya faru, sannan kuma za a birne gawarwakin da suka rube a wurin.”

A watan da ya gabata, mutane biyu aka kashe tare da daidaita iyalai 475 a wani hari da mayakan Boko Haram suka kai wanda ya shafi mutum 2,390 a gundumar Mafa.

Kara karanta wannan

Kebbi: APC ta mayar da martani bayan sanar da sakamakon zaben ƙananan hukumomi

Boko Haram ta kai hari Yobe

Tun da fari, Tun da fari, Legit Hausa ta ruwaito cewa 'yan ta'addan Boko Haram sun kashe gomman mutane a harin da suka kai Mafa da ke jihar Yobe.

An ce ‘yan ta’addan na Boko Haram sun kashe mutanen kauyen da dama, musamman manoma, tare da kona gidaje da shaguna a garin da ke karamar hukumar Tamuwa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.