Sojoji Sun Cafke Masu Kai Wa ‘Yan Ta'adda Miyagun kwayoyi a Arewa Maso Gabas

Sojoji Sun Cafke Masu Kai Wa ‘Yan Ta'adda Miyagun kwayoyi a Arewa Maso Gabas

  • Rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa (MNJTF) ta yi nasarar cafke mutane biyu da ake zargi da kai wa 'yan ta'adda miyagun kwayoyi
  • Rundunar ta bayyana cewa an kama mutanen a hanyar Kekeno zuwa Cross Kauwa a jihar Borno kuma a kwato kwayoyi da tabar wiwi
  • Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, kakakin rundunar MNJTF ya kara da cewa sojojin sun ceto wasu mata uku da jaririn a yayin atisayen

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Borno - Rundunar sojojin hadin gwiwa ta MNJTF ta ce ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa mayakan Boko Haram da ISWAAP miyagun kwayoyi a yankin tafkin Chadi.

Kara karanta wannan

Kwalliya ta zo da gardama: Budurwa ta sheka lahira a wajen tiyatar karin mazaunai

An kuma yi zargin cewa wadanda aka kaman suna safarar kakin jami'an tsaro da wasu kayayyaki ga 'yan ta'addan.

Sojoji sun kama masu kai wa 'yan ta'adda miyagun kwayoyi
Borno: Masu kai wa 'yan ta'adda miyagun kwayoyi sun shiga hannun sojoji. Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

An cafke aminan 'yan Boko Haram

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, kakakin rundunar MNJTF ya fitar ranar Alhamis a Maiduguri, a cewar rahoton Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce dakarun rundunar sun kama daya daga cikin wadanda ake zargin a kan hanyar Kekeno zuwa Cross Kauwa a jihar Borno.

Laftanar Kanal Olaniyi ya kara da cewa dakarun sun kwato kwato kayayyakin maye masu yawa da kuma kunshin tabar wiwi 198.

Borno: An ceto mata da jariri

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa kakakin rundunar ya ce sojojin sun kuma ceto mata uku da jariri daya, wadanda ake zargin 'yan uwa ne ga 'yan ta'addar.

A cewarsa, matan sun yi ikirarin cewa sun tsero ne daga mabuyar ‘yan ta’addan a kudancin tsibirin Tafkin Chadi a karamar hukumar Marte a jihar Borno.

Kara karanta wannan

Kano: NSCDC ta hannatawa kotu da NCC kayayyakinsu da aka sace lokacin zanga zanga

“A halin yanzu ana duba lafiyar matan da jaririn tare da kuma tattara bayanansu."

- A cewar Laftanar Kanal Olaniyi.

An kama makusantan 'yan ta'adda

A wani labarin, mun ruwaito cewa rundunar sojojin hadin gwiwa ta MNJTF ta ce dakarunta sun kama iyalai da masu taimakawa mayakan Boko Haram.

Rundunar ta ce an kama aklla mutane 900 da ke da alaka da 'yan ta'addan yayin da dakarunta ke ci gaba da karya lagon 'yan Boko Haram da ISWAP a yakin Tafkin Chadi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.