Yadda Zanga Zanga Ta Hana Gwamnati Kara Kudin Wuta, Ministan Tinubu Ya Magantu

Yadda Zanga Zanga Ta Hana Gwamnati Kara Kudin Wuta, Ministan Tinubu Ya Magantu

  • Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ana kashe Naira 120 domin samar da kilowatt 1 na wutar lantarki a kowacce awa
  • Ministan wutar lantarki, Cif Adebayo Adelabu wanda ya bayyana hakan ya ce kudin da 'yan Najeriya ke biya na wuta ya kasa
  • A cewar ministan, ma'aikatar wuta ta yi niyyar gabatar da sabon karin kudin wutar amma zanga-zangar da aka yi ta kawo cikas

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Ministan wutar lantarki, Cif Adebayo Adelabu, ya ce ana kashe N120 domin samar da kilowatt 1 na wutar lantarki a kowacce awa.

Cif Adebayo ya yi nuni da cewa wannan dalilin ne ya sa gwamnatin tarayya ke kashe kudade masu yawa wajen biyan tallafin wutar.

Kara karanta wannan

Tinubu ya dauko muhimmiyar hanyar inganta lantarki, NERC ta ba MTN izini

Ministan wutar lantarki ya yi magana kan kudin da ake kashewa wajen samar da wuta
Minista Adebayo Adelabu ya fadi dalilin janye batun kara kudin wutar lantarki. Hoto: @deeduke1
Asali: Twitter

Ya yi wannan jawabi ne a wata ziyarar sa-ido da ‘yan majalisar wakilai kan harkokin wutar lantarki suka kai ofishinsa da ke Abuja, inji rahoton The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnati ta magantu kan samar da wuta

Ministan ya ce kudin bai hada da sauran kudaden da kamfanonin rarraba wutar lantarki ke biya ba a masana’antar samar da wuta ta Najeriya (NESI).

“Wadanda ke a 'Band A' suna biyan N209 yayin da 'Band B' ke biyan N65. Amma kudin da ake samar da kilowat 1 kowacce awa ba ya gaza N120.
"Don haka duk wanda ke biyan N65 ko N58 yana biyan kasa da kudin da gwamnatin tarayya ke bayarwa na tallafin kudin wutar."

- A cewar Cif Adebayo.

Zanga-zanga ta hana kara kudin wuta

Jaridar Daily Trust ta ruwaito ministan ya kara da cewa idan ba domin zanga-zangar da aka yi a baya-bayan nan ba, da ma’aikatar ta kara kudin wuta ga 'yan kasar.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai farmaki, sun yi garkuwa da daliban kwalejin kiwon lafiya

“Watakila nan da watanni 6 masu zuwa, za mu iya zuwa wurin shugaban kasa mu gabatar da sabon tsari na kayyade kudin wutar, amma dai ba mu tsayar da lokaci ba.
“Ba a jima da gama zanga-zangar yunwa a fadin kasar ba, kuma ba ma son wani abu da zai jawo wata zanga-zangar don haka za mu jinkirta."

- A cewar ministan.

Gwamnati ta magantu kan rage kudin wuta

A wani labarin, mun ruwaito cewa ministan wutar lantarki, Cif Adebayo Adelabu ya ba da sharadi na janye karin kudin wutar lantarki da aka yi.

Ya bayyana cewa N225 a kowanne kilowat da masu amfani da lantarki ke biya a rukunin Band A zai ragu idan farashin dala ya dawo kasa da N1,000.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.