Ana Cikin Surutu, Gwamnati Ta Jero Kuɗin da Ake Turawa Kowane Sanata duk Wata

Ana Cikin Surutu, Gwamnati Ta Jero Kuɗin da Ake Turawa Kowane Sanata duk Wata

  • Gwamnatin tarayya ta bakin hukumar raba kudin shiga watau (RMAFC) ta bayyana albashin da kowane sanata yake samu
  • Hukumar ta karyata ikirarin da Sanata Shehu Sani ya yi na cewa kowane sanata na karbar N13.5m matsayin kudin gudanarwa a wata
  • A cewar hukumar RMAFC, albashin sanatoci bai kai kudin da Shehu Sani ya fadi ba, yayin da ta yi bayanin abin da ake biyan a majalisu

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Hukumar tattara kudaden shiga da kasafin kudi (RMAFC) ta yi karin haske kan albashin da 'yan majalisar dattawa ke karba a kowanne wata.

Hukumar RMAFC ta ce kowanne sanata daga cikin sanatoci 109 da ke a majalisar dattawa na karbar albashi da alawus na ₦1,063,860 a duk wata.

Kara karanta wannan

An nemi makiyaya 11 da shanu 33 an rasa a wata jihar Kudu, Miyetti Allah ta koka

Hukumar RMAFC ta bayyana kudaden da ake turawa sanatoci a duk wata
Gwamnati ta yiwa Shehu Sani martani, ta fadi albashin da kowane sanata ke dauka a wata. Hoto: @NGRSenate
Asali: Facebook

Shugaban RMAFC, M. B. Shehu, a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, ya yi wannan karin hasken matsayin martani ga wani ikirari na Sanata Shehu Sani, inji rahoton Channels.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"N14.25m ne albashin sanatoci" - Shehu Sani

Shehu Sani, wanda tsohon sanata ne daga Kaduna ya ce kowanne sanata na karbar kudin tafiyar da aiki a da ya kai N13.5m ban da N750,000.00 da hukumar RMAFC ke biya duk wata.

The Punch ta ruwaito Sanata Shehu ya ce hukumar RMAFC ba ta da wani karfin iko da tsarin mulki ya ba ta na tilasta albashi da alawus din da 'yan majalisar ke samu.

"Duk da haka, majalisar tarayya na kan warware wannan dambarwar da aka samu."

- In ji tsohon sanatan.

Hukumar RMAFC ta fadi albashin sanatoci

Shugaban RMAFC ya ce wasu alawus-alawus na yau da kullun ne yayin da wasu kuma na lokaci daya ne, yana mai cewa:

Kara karanta wannan

Gwamnatin tarayya ta nunka albashin ma'aikatan shari'a sau 3, Tinubu ya sanya hannu

“Ana biyan alawus-alawus na yau da kullun tare da albashi yayin da ake biyan alawus na lokaci daya a dukkanin lokacin da bukatar hakan ta taso.
"Misali, alawus na kujeru, tebura da sauran kayan gida (N6,079,200) da alawus na sallamar aiki (N6,079,200) ana biyansu sau daya a shekaru hudu."

Hukumar RMAFC ta kara da cewa ana biyan kowane sanata N8,105,600 na alawus din sayen mota wanda ke zuwa matsayin rance da dan majalisar ke biya kafin barin ofis.

Nawa ne kudin sanatoci duk wata?

Hukumar ta bayar da bayanin albashi da kuma alawus da ake biyan kowane sata a duk wata kamar haka:

  • Albashi - N168,866:70
  • Kudin fetur da kula da abin hawa - N126,650:00
  • Kudin biyan hadimai - N42,216:66
  • Kudin biyan 'yan aikin gida - N126,650:00
  • Kudin nishadi - N50,660:000
  • Kudin ruwa, wuta da sauran ayyuka - N50,660:00
  • Kudin jarida - N25,330:00
  • Kudin sutura - N42,216:00
  • Kudin kula da gida - N8,443:33
  • Kudin ayyukan mazaba - N422,166:66

Kara karanta wannan

El-Rufai ya sake burmawa matsala da ake zargin mutuminsa kan zambar N11bn

"An karawa sanatoci albashi" - Jaafar Jaafar

A wani labarin, mun ruwaito cewa fitaccen ‘dan jaridar nan daga Kano, Ja’afar Ja’afar ya yi ikirarin cewa an kara albashin da ‘yan majalisar tarayya suke karba.

Ja’afar Ja’afar ya yi wannan magana ne a shafukansa na sada zumunta inda ya yi ikirarin cewa sanatan da ake biya N13.5m a kowane wata, yanzu ya koma karbar N20m.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.