Ta Faru ta Kare, Manyan Arewa Sun Hakura da Shiga Zanga Zanga, Sun ba Matasa Shawara

Ta Faru ta Kare, Manyan Arewa Sun Hakura da Shiga Zanga Zanga, Sun ba Matasa Shawara

  • Kungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) ta ce ba za ta shiga cikin zanga-zangar yunwa da ake shirin farawa daga ranar Alhamis ba
  • Kungiyar manyan Arewan ta yi nuni da cewa manufar zanga-zangar ba ta shafi babbar matsalar tsaro da ta addabi yankin Arewa ba
  • A yayin da ta zayyana dalilanta na kin shiga zanga-zangar, ta yi kira ga gwamnati da ta dauki matakan kawo sauki ga rayuwar 'yan kasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Kungiyar manyan Arewa ta ACF ta tsame hannunta daga zanga-zangar da aka shirya gudanarwa na tsawon kwanaki 10 a fadin kasar nan.

Sanarwar matsayar Arewa Consultative Forum kan zanga-zangar ta fito ne ta hannun Farfesa Tanko Muhammad-Baba, sakataren yada labaran kungiyar na kasa.

Kara karanta wannan

Ohanaeze: Dalilin da ya sa matasan Ibo ba za su shiga zanga zangar yunwa ba

Kungiyar Arewa Consultative Forum ta yi magana kan zanga-zangar yunwa
Arewa Consultative Forum ta kauracewa zanga-zangar da ake shirin farawa a ranar Alhamis. Hoto: Uba Sani
Asali: Facebook

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai, Bayo Onanuga ne ya wallafa sanarwar a shafinsa na X a ranar Talata, 30 ga Yulin 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Manyan Arewa sun fice daga zanga-zanga

Sanarwar ACF ta ce:

“Kungiyar ACF ta sa ido sosai a kan manufofin da suke tattare da shirya zanga-zangar yunwa, wadda wasu da ba a san ko su waye ba za su jagoranta.
“Bayanan da ke yawo a intanet sun danganta zanga-zangar da rashin gamsuwa da tsadar rayuwa da ta addabi kasar sakamakon wasu tsare-tsaren gwamnatin Bola Tinubu.
"Yayin da take amincewa da 'yancin da tsarin mulki ya ba 'yan Najeriya na yin zanga-zanga, ACF ta yi hannun riga da wannan shiri na yin zanga-zangar yunwar."

Meyasa manyan Arewa hakura da zanga-zangar?

ACF ta zayyana dalilai da dama na adawa da zanga-zangar kamar rashin tuntubar manya game da rikon amana da gudanar da mulki da kuma rashin fayyace buƙatun masu zanga-zangar.

Kara karanta wannan

Ana sauran kwana 2, zanga zanga ta gamu da gagarumin koma baya a Arewa

Kungiyar ta kara da cewa kai tsaye wannan zanga-zangar ba ta kawo wata mafita ta magance matsalar rashin tsaro a Arewa ba.

Jaridar Vanaguard ta ruwaito ACF na cewa:

"Rufe kasar na kwanaki 10 zai wuce kima kuma ba zai yi tasiri ba, wanda akwai yuwuwar zanga-zangar ta rikide zuwa tashin hankali ko kuma 'yan ta'adda su fake da ita."

ACF ta bukaci matasa da su guji shiga zanga-zangar tare da yin kira ga gwamnati da ta saurari koken jama'a domin magance manyan matsalolin da suka addabi kasar.

Matasan Ibo sun kauracewa zanga-zanga

A wani labarin, mun ruwaito cewa matasan Ibo sun yanke shawarar ficewa daga cikin shirin zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a farkon watan Agusta.

Kungiyar Ibo ta Ohanaeze Ndigbo ce ta sanar da hakan bayan ganawa da matasan kan matsalolin shiyyar Kudu maso Gabas.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.