Bello Turji Ya Fadi Yadda Ta’addanci Ya Fara a Arewa, Ya Jefa Tsohon Gwamna a Matsala
- Ƙasurgumin ɗan ta'adda, Muhammad Bello Turji ya bayyana yadda aka fara ayyukan ta'addanci a Arewa maso yammacin Najeriya
- Ɗan ta'addan ya ce tun asali suna zaman lafiya a yankin amma sai wasu abubuwa suka faru wanda sune suka jawo barkewar ta'addanci
- Bello Turji ya bayyana haka ne bayan wani mutum ya masa tambaya a kan ya bayar da tarihin ta'addanci a yankin a matsayinsa na shugaba
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Zamfara - Jagoran 'yan ta'adda a Arewa maso yammacin Najeriya, Bello Muhammad Turji ya bayyana abin da ya jawo ta'addanci a yankin.
Bello Turji ya zargi tsohon gwamnan jihar Zamfara, Ahmed Sani Yariman Bakura da ɗaukan matakin da ya tayar da fitinar.
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/d6eb4781e43a3c84.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
Sanusi II Vs Aminu: An fara zaman ɗari ɗari a Kano bayan hukuncin da kotu ta yanke
![Bello Turji Bello Turji](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/5d9e2031698089af.jpg?imwidth=900)
Asali: Facebook
Legit ta tatttaro bayanan ne cikin wani bidiyo da Bello Turji ya amsa tambaya kamar yadda Price Abdulmalik Shehu Sfada ya wallafa a kafar Facebook.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Turji ya ce da farko ana lafiya
A cikin bidiyon, Bello Turji ya ce a farkon lamari ana zaman lafiya tsakanin Hausawa da Fulani a yankunan jihar Zamfara.
Turji ya ce ana cikin zaman lafiya sai aka yi zabe, Allah ya ba Alhaji Ahmed Sani Yarima nasarar zama gwamna a jihar Zamfara.
Yarima ya kawo shari'a Zamfara
'Dan ta'addan ya yi ikirarin Ahmed Sani Yariman Bakura ya kirkiro shari'a a Zamfara ne domin ya muzgunawa 'yan ƙabilar Fulani.
Saboda haka ne ma ya ce an fara yanke hannun Bafulatani da ya yi sata amma ba a kara hukunta wani a fadin jihar Zamfara ba.
'Yan banga sun sa Fulani a gaba
Biyo bayan yanke hannun Bafulatani ne Bello Turji ya ce sai yan banga da yan sa kai suka rika cin karensu babu babbaka a kan Fulani.
Bello Turji ya ce a lokacin maimakon gwamnati da sauran al'umma su dakatar da su amma sai kowa ya kawar da kai.
Kuma a karkashin haka ne suma suka dauki makami domin kare kansu da samawa yan uwansu 'yanci.
Bello Turji ya sako mutane
A wani rahoton, kun ji cewa hatsabibin shugaban ƴan bindigan nan Bello Turji ya sako wasu mutum 20 da yaransa suka yi garkuwa da su a jihar Zamfara.
A cewar mutanen da aka sako ɗin, Bello Turji ya bayar da umarnin sako su ne saboda ƙoƙarin sulhu da wasu jami'an gwamnati daga Abuja suka fara.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng