Yadda Aka Yi Hasashen Dawowar Sanusi II Kuma Ta Tabbata Bayan Kwanaki 1538

Yadda Aka Yi Hasashen Dawowar Sanusi II Kuma Ta Tabbata Bayan Kwanaki 1538

  • Muhammadu Sanusi II ya sake komawa gadon sarautar dabo, bayan an shafe kwanaki 1538 da cire masa rawani
  • Hassan Sani Tukur yana cikin masu ba gwamna Abba Kabir Yusuf shawara, a 2023 ya yi hasashen rana irin Juma’a
  • Kamar yadda Hassan ya yi magana a X a shekarar 2023, ranar Juma’ar da ya fada ne aka cikawa masoya burinsu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Kano - Yanzu maganar da ake yi, Muhammadu Sanusi II shi ne sarkin Kano, shekaru hudu kenan bayan an sauke shi daga kan mulki.

Dawowar Mai martaba kan karagar mulki bayan gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta gyara dokar masarautu ya jawo surutu iri-iri a yau.

Muhammadu Sanusi II
Muhammadu Sanusi II ya sake hawa gadon daba a Kano Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

Hassan ya ce Juma'a Sanusi II zai dawo

Kara karanta wannan

Gwamna Abba ya ɗauki zafi, ya ba da umarnin a kama tsohon Sarkin Kano

Legit Hausa ta ci karo da yadda daya daga cikin masu taimakawa gwamnan Kano, Abba Yusuf ya taba yin hasashen ranar nan a X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A watan Yunin 2023, Hassan Sani Tukur mai taimakawa gwamna a bangaren kafofin sadarwa na zamani ya nuna Khalifa zai dawo.

“A ranar Juma’a, da yardar Ubangiji da ikonSa, za a tabbatar da burin mutanen Kano.” - Hassan Sani Tukur

Sanusi II: Maganar da aka yi ta tabbata

Malam Hassan Sani Tukur ya yi hannunka mai sanda ne a lokacin, sakon nasa yana dauke da alamar rawani da ke nufin gidan sarauta.

Masu bibiyarsa a lokacin sun fahimci ana nufin za a maido Muhammadu Sanusi II mulki ko kuwa akalla a soke karin masarautun Kano.

Hasashen Adeniyi, Omojuwa kan Sanusi II

Olusegun Adeniyi wanda ya yi aiki a matsayin mai magana da yawun bakin Ummaru Yar’adua ya ce san za a ga rana irin ta yau.

Kara karanta wannan

Sanusi II ya aika sako ga Ganduje bayan ya dawo kan sarautar Kano

A shafinsa na X, Mista Adeniyi ya dawo da wani tsohon rubutu da ya yi a This Day lokacin da gwamnatin Kano ta tsige Sarki a 2020.

Japeth Omojuwa wanda ya saba sharhi a kan abubuwan yau da kullum, ya yi farin ciki da jin cewa Sanusi II ya koma gadon sarauta.

A X, shi ma Omojuwa ya nuna dama can mai martaba zai sake zama sarki kuma a karshe sai gwamnati ta tsige sauran sarakuna.

Kwankwaso ya yi maganar Sanusi II

Ana da labari Rabiu Kwankwaso ya ce idan ya zo Kano, zai nemi bayanin yadda gwamnatin Abba Yusuf ta taba masarautu ba.

Rabiu Kwankwaso ya ce ba shi ya sa Abba ya sake naɗa Muhammadu Sanusi II ba amma zai bincika domin fahimtar abin da ya faru.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

Online view pixel