Kotu Ta Dakatar da Gwamnatin Kano Daga Mayar da Sanusi II Gidan Sarauta

Kotu Ta Dakatar da Gwamnatin Kano Daga Mayar da Sanusi II Gidan Sarauta

  • Babbar kotun tarayya da ke Kano ta bayar da umarnin hana gwamnatin jihar Kano aiwatar da dokar rushe majalisar masarautar Kano
  • Mai shari’a Mohammed Liman ne ya yanke hukuncin a kan bukatar da wani basarake, Alhaji Aminu Babba Dan Agundi ya shigar
  • Kotun ta umurci wadanda ake karar da su dakata da aiwatar da dokar rusa sarakunan har zuwa lokacin da za a kammala sauraron shari'ar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jihar Kano - Watakila Muhammadu Sanusi II ba zai shiga gidan sarauta yanzu ba yayin da babbar kotun tarayya ta dakatar da gwamnatin Kano daga nada sabon sarki.

Kotun Mai shari’a Liman ta bayar da umurnin hana gwamnatin jihar Kano mayar da Sarki Muhammadu Sanusi II kan karagar mulki.

Kara karanta wannan

Sarkin Kano: Duk da umarnin kotu, Gwamna Abba zai mika takardar nadi ga Sanusi II

Kotu ta yi hukunci kan batun nada sabon sarki a Kano
Kotu ta dakatar da nada sabon sarki a Kano. Hoto: @masarautarkano, @Kyusufabba
Asali: Facebook

Jaridar Daily Nigerian ta tattaro cewa alkalin ya bada umarnin ne a daren ranar Alhamis duk da cewa a halin yanzu yana kasar Amurka.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sarkin Dawaki Babba ya shigar da kara

Wani mai rike da sarautar gargajiya, Sarkin Dawaki Babba, Aminu Babba-Dan’Agundi ne ya shigar da kara gaban kotun ta dakatar da nadin sabon sarkin.

Wadanda ake kara a cikin shari’ar sun hada da: gwamnatin jihar Kano, majalisar dokoki, shugaban majalisa da babban lauyan gwamnatin Kano.

Sauran sun hada da: Kwamishinan ‘yan sanda, Sufeto-Janar na ‘yan sanda (IGP), jami’an tsaro na NSCDC da SSS ta jihar Kano.

Kotu ta dakatar da nada sabon sarki

Kotun ta bayar da umarnin a mika duk wasu takardu ko bayanan shari’a a kan IGP a Abuja, wanda ke wajen hurumin kotun, jaridar The Nation ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Dalilin da ya sa Gwamna Abba ya mayar da Sanusi II kan kujerar Sarkin Kano

Kotun ta umurci wadanda ake karar da su dakata da aiwatar da dokar rusa sarakunan har zuwa lokacin da za a kammala sauraron shari'ar.

Kotun za ta fara yin zama domin sauraron bangarorin da shari'ar ta shafa kan tauye hakki a ranar 3 ga watan Yuni, 2024.

Abba ya yi magana kan nada Sanusi II

Tun da fari, mun ruwaito cewa Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya bayyana cewa maida tsohon Sarkin Kano, Lamido Sanusi kan karaga, cika alkawari ne na yakin neman zabe.

A ranar Alhamis ne Gwamna Yusuf ya tsige Aminu Ado Bayero a matsayin Sarkin Kano tare da mayar da Sanusi II a matsayin Sarkin Kano na 16.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel