Gwamna Abba Ya Sa Labule da 'Yan Majalisa, Masu Nada Sarki a Kano, Bayanai Sun Fito
- Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanya labule da ƴan majalisar dokokin jihar da masu naɗa sabon Sarki
- Ganawar gwamnan da mutanen na zuwa ne bayan majalisar dokokin jihar ta amince da sabon ƙudirin dokar da ya yi wa dokar kafa masarautun jihar garambawul
- Ana sa ran Gwamna Abba zai rattaɓa hannu a dokar wacce ta rushe sababbin masarautun da aka ƙirƙiro a lokacin mulkin tsohon gwamna Abdullahi Umar Ganduje
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Kano - Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya shiga ganawar sirri da ƴan majalisar dokokin jihar a gidan gwamnatin jihar.
A ganawar da gwamnan ya shiga har da wasu masu riƙe da sarautun gargajiya da ake kyautata zaton masu naɗa Sarki ne.
![Gwamna Abba ya gana da 'yan majalisa a Kano Gwamna Abba ya gana da 'yan majalisa a Kano](https://cdn.legit.ng/images/1120/37f729d2c925a61d.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Ana sa ran gwamnan zai sanya hannu kan ƙudirin dokar da majalisar dokokin jihar ta amince da shi tun farko a ranar Alhamis wanda ya rushe sababbin masarautu da gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ta ƙirƙiro.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Muhammad Sanusi II zai zama sabon Sarki
Idan Gwamna Abba ya sanya hannu kan wannan ƙudirin dokar, ana sa ran za a dawo da Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II, wanda aka tsige a watan Maris ɗin 2020, cewar rahoton tashar Channels tv.
Sai dai har yanzu ba a san makomar Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero ba.
Rahotanni sun ce Sarki Aminu Ado Bayero ba ya Kano a halin yanzu bayan da ya ziyarci Oba Sikiru Adetona, Awujale na Ijebuland, a ranar Laraba.
Gwamnatin Rabiu Kwankwaso ta nada Muhammad Sanusi II, tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), a matsayin Sarkin Kano na 14 a watan Yunin 2014.
Gwamna Abba ya rushe masarautun Kano
A wani labarin kuma, kun ji cewa Gwamna Abba Kabir na jihar Kano ya sanya hannu kan dokar da ta rusa masarautun jihar.
Gwamnan ya sanya hannun ne a ranar Alhamis, 23 ga watan Mayu bayan mika masa takarda mai ɗauke da dokar a gidan gwamnatin jihar.
Rattaba hannu kan dokar ya sake tabbatar da rushe masarautun guda biyar da gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ta ƙirƙiro.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng